Fassarar Surar An-Naba'i a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﭑﭒ
ﭓ
An-Naba'i
A kan mẽ suke tambayar jũna?
Verse 2
ﭔﭕﭖ
ﭗ
A kan muhimmin lãbãri mai girma (Alƙur'ãni)?
Verse 3
ﭘﭙﭚﭛ
ﭜ
Wanda suke sãɓa wa jũna a cikinsa?
Verse 4
ﭝﭞ
ﭟ
A'aha! Zã su sani.
Verse 5
ﭠﭡﭢ
ﭣ
Kuma, a'aha! Zã su sani.
Verse 6
ﭤﭥﭦﭧ
ﭨ
Ashe, ba Mu sanya ƙasa shimfiɗa ba?
Verse 7
ﭩﭪ
ﭫ
Da duwãtsu turaku (ga riƙe ƙasa)?
Verse 8
ﭬﭭ
ﭮ
Kuma, Mun halitta ku mazã da mãtã?
Verse 9
ﭯﭰﭱ
ﭲ
Kuma, Muka sanya barcinku hũtãwa?
Verse 10
ﭳﭴﭵ
ﭶ
Kuma, Muka sanya dare (ya zama) sutura?
Verse 11
ﭷﭸﭹ
ﭺ
Kuma, Muka sanya yini (yazama) lõkacin nẽman abinci?
Verse 12
ﭻﭼﭽﭾ
ﭿ
Kuma, Muka gina, a samanku, sammai bakwai mãsu ƙarfi?
Verse 13
ﮀﮁﮂ
ﮃ
Kuma, Muka sanya fitila mai tsanin haske (rãnã)?
Verse 14
ﮄﮅﮆﮇﮈ
ﮉ
Kuma, Muka saukar daga cikakkun girãgizai, ruwa mai yawan zuba?
Verse 15
ﮊﮋﮌﮍ
ﮎ
Dõmin, Mu fitar da ƙwaya da tsiri game da shi?
Verse 16
ﮏﮐ
ﮑ
Da itãcen lambuna mãsu lillibniya?
Verse 17
ﮒﮓﮔﮕﮖ
ﮗ
Lalle ne, rãnar rarrabẽwa tã kasance abin ƙayyadẽ wa lõkaci.
Verse 18
ﮘﮙﮚﮛﮜﮝ
ﮞ
Rãnar da zã a yi bũsa a cikin ƙaho, sai ku zo, jama'a jama'a.
Verse 19
ﮟﮠﮡﮢ
ﮣ
Kuma, aka buɗe sama, sai ta kasance ƙõfõfi.
Verse 20
ﮤﮥﮦﮧ
ﮨ
Kuma, aka tafiyar da duwãtsu, sai suka kasance ƙũra.
Verse 21
ﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
Lalle ne, Jahannama tã kasance madãkata.
Verse 22
ﮮﮯ
ﮰ
Ga mãsu ƙẽtare iyãkõki, tã zama makõma.
Verse 23
ﮱﯓﯔ
ﯕ
Sunã, mãsu zama a cikinta, zãmunna.
Verse 24
ﯖﯗﯘﯙﯚﯛ
ﯜ
Bã su ɗanɗanãwar wani sanyi a cikinta, kuma bã su ɗanɗana abin sha.
Verse 25
ﯝﯞﯟ
ﯠ
Fãce tafasasshen ruwa da ruɓaɓɓen jini.
Verse 26
ﯡﯢ
ﯣ
Sakamako mai dãcẽwa.
Verse 27
ﯤﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
Lalle ne, sũ, sun kasance bã su fãtar sauƙin wani hisãbi.
Verse 28
ﯪﯫﯬ
ﯭ
Kuma, suka ƙaryata game da ãyõyinMu, ƙaryatãwa!
Verse 29
ﯮﯯﯰﯱ
ﯲ
Alhãli, kõwane abu Mun ƙididdigẽ shi, a rubũce.
Verse 30
ﯳﯴﯵﯶﯷ
ﯸ
Sabõda haka, ku ɗanɗana domin haka, bã zã Mu ƙara muku kõme ba fãce azãba.
Verse 31
ﭑﭒﭓ
ﭔ
Lalle ne, mãsu taƙawã nã da wani wurin sãmun babban rabo.
Verse 32
ﭕﭖ
ﭗ
Lambuna da inabõbi.
Verse 33
ﭘﭙ
ﭚ
Da cikakkun 'yammata, tsãrar jũna.
Verse 34
ﭛﭜ
ﭝ
Da hinjãlan giya cikakku.
Verse 35
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣ
ﭤ
Bã su jin yãsassar magana, a cikinta, kuma bã su jin ƙaryatãwa.
Verse 36
ﭥﭦﭧﭨﭩ
ﭪ
Dõmin sakamako daga Ubangijinka, kyautã mai yawa.
Verse 37
Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, Mai rahama, bã su da ikon yin wata magana daga gare Shi.
Verse 38
Rãnar da Rũhi da malã'iku zã su tsaya a cikin safu, bã su magana, sai wanda Allah Ya yi masa izni, kuma ya faɗi abin da ke daidai.
Verse 39
Wancan, shi ne yini na gaskiya; to wanda ya so, ya riƙa makõma zuwa ga Ubangijinsa.
Verse 40
Lalle ne, Mũ, Mun yi muku gargaɗin azãba makusanciya, rãnar da mutum ke dũbi zuwa ga abin da hannãyensa suka aikata, kuma kafiri ya ce: "Kaitona, dã dai nã zama turɓãya!"
تقدم القراءة