سورة الواقعة

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Fassarar Surar Al-Waki'ah a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Verse 3

(Ita) mai ƙasƙantãwa ce, mai ɗaukakãwa.
Verse 10

Da waɗanda suka tsẽre. Sũ wɗanda suka tsẽren nan,
Verse 11

Waɗancan, sũ ne waɗanda aka kusantar.
Verse 16

Sunã gincire a kansu, sunã mãsu kallon jũna.
Verse 20

Da wasu 'ya'yan itãcen marmari daga irin waɗanda suke zãɓe.
Verse 22

Da wasu mãtã mãsu fararen idanu da girmansu.
Verse 24

A kan sakamakon, dõmin abin da suka kasance sunã aikatãwa.
Verse 32

Da wasu 'ya'yan itacen marmari mãsu yawa.
Verse 37

Mãsu son mazansu, a cikin tsãrã ɗaya.
Verse 42

Sunã a cikin wata iskar zãfi da wani ruwan zãfi.

Kuma sun kasance sunã cẽwa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓãya da ƙasũsuwa shin lalle mũ waɗanda zã a kõma rãyarwa ne haƙĩƙatan?"
Verse 48

"Shin, kuma da ubanninmu na farko?"
Verse 53

"Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."
Verse 54

"Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."
Verse 55

"Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."
Verse 58

Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?

Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?

Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.
Verse 66

(Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"

Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.
Verse 77

Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja.
Verse 82

Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)?
Verse 83

To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa).
Verse 84

Alhãli kuwa kũ, a lõklcin nan, kunã kallo.
Verse 87

Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya.
Verse 96

Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangijinka, Mai karimci.
تقدم القراءة