Fassarar Surar Al-Waki'ah a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﮃﮄﮅ
ﮆ
Al-Waki'ah
Idan mai aukuwa ta auku.
Verse 2
ﮇﮈﮉ
ﮊ
Bãbu wani (rai) mai ƙaryatãwa ga aukuwarta.
Verse 3
ﮋﮌ
ﮍ
(Ita) mai ƙasƙantãwa ce, mai ɗaukakãwa.
Verse 4
ﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
Idan aka girgiza ƙasã girgizwa.
Verse 5
ﮓﮔﮕ
ﮖ
Kuma aka niƙe duwãtsu, niƙẽwa.
Verse 6
ﮗﮘﮙ
ﮚ
Sai suka kasance ƙũra da ake wãtsarwa.
Verse 7
ﮛﮜﮝ
ﮞ
Kuma kun kasance nau'i uku.
Verse 8
ﮟﮠﮡﮢﮣ
ﮤ
Watau mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?
Verse 9
ﮥﮦﮧﮨﮩ
ﮪ
Da mazõwa hagu. Mẽne ne mazõwa hagu?
Verse 10
ﮫﮬ
ﮭ
Da waɗanda suka tsẽre. Sũ wɗanda suka tsẽren nan,
Verse 11
ﮮﮯ
ﮰ
Waɗancan, sũ ne waɗanda aka kusantar.
Verse 12
ﮱﯓﯔ
ﯕ
A ckin Aljannar ni'ima.
Verse 13
ﯖﯗﯘ
ﯙ
Jama'a ne daga mutãnen farko.
Verse 14
ﯚﯛﯜ
ﯝ
Da kaɗan daga mutãnen ƙarshe.
Verse 15
ﯞﯟﯠ
ﯡ
(Sunã) a kan wasu gadãje sãƙaƙƙuu.
Verse 16
ﯢﯣﯤ
ﯥ
Sunã gincire a kansu, sunã mãsu kallon jũna.
Verse 17
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Wasu yara samãri na dindindin gẽwaya a kansu.
Verse 18
ﭖﭗﭘﭙﭚ
ﭛ
Da wasu kõfuna da shantula da hinjãlai daga (giya) mai ɓuɓɓuga.
Verse 19
ﭜﭝﭞﭟﭠ
ﭡ
Bã a sanya musu cĩwon jirĩ sabõda ita, kuma bã su buguwa.
Verse 20
ﭢﭣﭤ
ﭥ
Da wasu 'ya'yan itãcen marmari daga irin waɗanda suke zãɓe.
Verse 21
ﭦﭧﭨﭩ
ﭪ
Da nãman tsuntsãye daga wanda suke ganin sha'awa.
Verse 22
ﭫﭬ
ﭭ
Da wasu mãtã mãsu fararen idanu da girmansu.
Verse 23
ﭮﭯﭰ
ﭱ
Kamar misãlan lu'ulu'u wanda aka ɓõye.
Verse 24
ﭲﭳﭴﭵ
ﭶ
A kan sakamakon, dõmin abin da suka kasance sunã aikatãwa.
Verse 25
ﭷﭸﭹﭺﭻﭼ
ﭽ
Bã su jin wata yãsassar magana a cikinta, kuma bã su jin sun yi laifi.
Verse 26
ﭾﭿﮀﮁ
ﮂ
Sai dai wata magana (mai dãɗi): Salãmun, Salãmun.
Verse 27
ﮃﮄﮅﮆﮇ
ﮈ
Da mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma?
Verse 28
ﮉﮊﮋ
ﮌ
(Sunã) a cikin itãcen magarya maras ƙaya.
Verse 29
ﮍﮎ
ﮏ
Da wata ayaba mai yawan 'ya'ya.
Verse 30
ﮐﮑ
ﮒ
Da wata inuwa mĩƙaƙƙiya.
Verse 31
ﮓﮔ
ﮕ
Da wani ruwa mai gudãna.
Verse 32
ﮖﮗ
ﮘ
Da wasu 'ya'yan itacen marmari mãsu yawa.
Verse 33
ﮙﮚﮛﮜ
ﮝ
Bã su yankẽwa kuma bã a hana su.
Verse 34
ﮞﮟ
ﮠ
Da wasu shimfiɗu maɗaukaka.
Verse 35
ﮡﮢﮣ
ﮤ
Lalle Mũ, Mun ƙãga halittarsu ƙãgãwa.
Verse 36
ﮥﮦ
ﮧ
Sa'an nan Muka sanya su budurwai.
Verse 37
ﮨﮩ
ﮪ
Mãsu son mazansu, a cikin tsãrã ɗaya.
Verse 38
ﮫﮬ
ﮭ
Ga mazõwa dãma.
Verse 39
ﮮﮯﮰ
ﮱ
Wata ƙungiya ce daga mutãnen farko.
Verse 40
ﯓﯔﯕ
ﯖ
Da wata ƙungiya daga mutãnen ƙarshe.
Verse 41
ﯗﯘﯙﯚﯛ
ﯜ
Mazõwa hagu, Mẽne ne mazõwa hagu?
Verse 42
ﯝﯞﯟ
ﯠ
Sunã a cikin wata iskar zãfi da wani ruwan zãfi.
Verse 43
ﯡﯢﯣ
ﯤ
Da wata inuwa ta hayãƙi mai baƙi.
Verse 44
ﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
Bã mai sanyi ba, kuma bã mai wata ni'ima ba.
Verse 45
ﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
Lalle sũ, sun kasance a gabãnin wannan waɗanda aka jiyar dãɗi.
Verse 46
ﯰﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Kuma sun kasance sunã dõgẽwa a kan mummũnan zunubi mai girma.
Verse 47
Kuma sun kasance sunã cẽwa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓãya da ƙasũsuwa shin lalle mũ waɗanda zã a kõma rãyarwa ne haƙĩƙatan?"
Verse 48
ﰀﰁ
ﰂ
"Shin, kuma da ubanninmu na farko?"
Verse 49
ﰃﰄﰅﰆ
ﰇ
Ka ce: "Lalle mutãnen farko da na ƙarshe."
Verse 50
ﰈﰉﰊﰋﰌ
ﰍ
"Tabbas, waɗanda ake tãrãwa ne a cikin wani yini sananne."
Verse 51
ﭑﭒﭓﭔﭕ
ﭖ
"Sa'an nan lalle ku, ya kũ ɓatattu, mãsu ƙaryatãwa!"
Verse 52
ﭗﭘﭙﭚﭛ
ﭜ
"Lalle mãsu cĩ ne daga wata itãciya ta zaƙƙum (ɗanyen wutã)."
Verse 53
ﭝﭞﭟ
ﭠ
"Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."
Verse 54
ﭡﭢﭣﭤ
ﭥ
"Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."
Verse 55
ﭦﭧﭨ
ﭩ
"Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."
Verse 56
ﭪﭫﭬﭭ
ﭮ
Wannan ita ce liyãfarsu a rãnar sakamako.
Verse 57
ﭯﭰﭱﭲ
ﭳ
Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba?
Verse 58
ﭴﭵﭶ
ﭷ
Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?
Verse 59
ﭸﭹﭺﭻﭼ
ﭽ
Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa?
Verse 60
Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa ba,
Verse 61
A kan Mu musanya waɗansu (mutãne) kamarku, kuma Mu mayar da ku a cikin wata halitta da ba ku sani ba.
Verse 62
ﮐﮑﮒﮓﮔﮕ
ﮖ
Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?
Verse 63
ﮗﮘﮙ
ﮚ
Shin, kuma kun ga abin da kũke nõmãwa?
Verse 64
ﮛﮜﮝﮞﮟ
ﮠ
Shin, kũ ne ke tsirar da shi kõ kuwa Mũ ne Mãsu tsirarwa?
Verse 65
ﮡﮢﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.
Verse 66
ﮨﮩ
ﮪ
(Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"
Verse 67
ﮫﮬﮭ
ﮮ
"Ã'a, mun dai zama waɗanda aka hanã wa!"
Verse 68
ﮯﮰﮱﯓ
ﯔ
Shin, kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha?
Verse 69
Shin, kũ ne kuke saukar da shi daga girgije, kõ kuwa Mũne Mãsu saukarwa?
Verse 70
ﯝﯞﯟﯠﯡﯢ
ﯣ
Dã Mun so, dã Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me bã ku gõdẽwa?
Verse 71
ﯤﯥﯦﯧ
ﯨ
Shin, kuma kun ga wutã wannan da kuke ƙyastãwa?
Verse 72
ﯩﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
Shin, kũ ne kuke ƙagã halittar itãciyarta, kõ kuwa Mũ ne Mãsu ƙãgãwa?
Verse 73
ﯰﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.
Verse 74
ﯶﯷﯸﯹ
ﯺ
Sai ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mai girma.
Verse 75
ﯻﯼﯽﯾﯿ
ﰀ
To, bã sai Na yi rantsuwa ba da lõkutan fãɗuwar taurãri.
Verse 76
ﰁﰂﰃﰄﰅ
ﰆ
Kuma lalle ne' haƙĩƙa, rantsuwa ce mai girma, dã kun sani.
Verse 77
ﭑﭒﭓ
ﭔ
Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja.
Verse 78
ﭕﭖﭗ
ﭘ
A cikin wani littafi tsararre.
Verse 79
ﭙﭚﭛﭜ
ﭝ
Bãbu mai shãfa shi fãce waɗanda aka tsarkake.
Verse 80
ﭞﭟﭠﭡ
ﭢ
Wanda aka saukar ne daga Ubangijin halitta.
Verse 81
ﭣﭤﭥﭦ
ﭧ
Shin, to, wannan lãbãrin ne kuke mãsu wulãkantãwa?
Verse 82
ﭨﭩﭪﭫ
ﭬ
Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)?
Verse 83
ﭭﭮﭯﭰ
ﭱ
To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa).
Verse 84
ﭲﭳﭴ
ﭵ
Alhãli kuwa kũ, a lõklcin nan, kunã kallo.
Verse 85
Kuma Mũ ne mafi kusanta gare shi daga gare ku, to, amma kũ bã ku gani.
Verse 86
ﭾﭿﮀﮁﮂ
ﮃ
To, don me in dai kun kasance bã waɗanda zã a yi wa sakamako ba?
Verse 87
ﮄﮅﮆﮇ
ﮈ
Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya.
Verse 88
ﮉﮊﮋﮌﮍ
ﮎ
To, amma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta,
Verse 89
ﮏﮐﮑﮒ
ﮓ
Sai hũtawa da kyakkyawan abinci da Aljannar ni'ima.
Verse 90
ﮔﮕﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
Kuma amma idan ya kasance daga mazõwa dãma,
Verse 91
ﮛﮜﮝﮞﮟ
ﮠ
Sai (a ce masa) aminci ya tabbata a gare ka daga mazõwa dãma.
Verse 92
ﮡﮢﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
Kuma amma idan ya kasance daga mãsu ƙaryatãwar, ɓatattun,
Verse 93
ﮨﮩﮪ
ﮫ
Sai wata liyãfa ta ruwan zãfi.
Verse 94
ﮬﮭ
ﮮ
Da ƙõnuwa da Jahĩm,
Verse 95
ﮯﮰﮱﯓﯔ
ﯕ
Lalle wannan, haƙĩƙa, ita ce gaskiya ta yaƙĩni.
Verse 96
ﯖﯗﯘﯙ
ﯚ
Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangijinka, Mai karimci.
تقدم القراءة