Fassarar Surar At-Tur a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﮞ
ﮟ
At-Tur
Inã rantsuwa da ¦ũr (Dũtsen Mũsã).
Verse 2
ﮠﮡ
ﮢ
Da wani littãfi rubũtacce.
Verse 3
ﮣﮤﮥ
ﮦ
A cikin wata takardar fãta shimfiɗaɗɗa.
Verse 4
ﮧﮨ
ﮩ
Da Gidan da aka rãyar da shi (da ibãda).
Verse 5
ﮪﮫ
ﮬ
Da rufin nan da aka ɗaukaka.
Verse 6
ﮭﮮ
ﮯ
Da tẽkun nan da aka cika (da ruwa).
Verse 7
ﮰﮱﯓﯔ
ﯕ
Lalle, azãbar Ubangijinka, haƙĩƙa, mai aukuwa ce.
Verse 8
ﯖﯗﯘﯙ
ﯚ
Bã ta da mai tunkuɗẽwa.
Verse 9
ﯛﯜﯝﯞ
ﯟ
Rãnar da samã ke yin mõtsi tanã kai kãwo.
Verse 10
ﯠﯡﯢ
ﯣ
Kuma duwãtsu nã tafiya sunã shũɗẽwa.
Verse 11
ﯤﯥﯦ
ﯧ
To, bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.
Verse 12
ﯨﯩﯪﯫﯬ
ﯭ
Waɗanda suke a cikin kududdufi sunã wãsã.
Verse 13
ﯮﯯﯰﯱﯲﯳ
ﯴ
Rãnar da zã a tunkuɗa su zuwa wutar Jahannama, tunkuɗãwa.
Verse 14
ﯵﯶﯷﯸﯹﯺ
ﯻ
(A ce musu): "Wannan ita ce wutar da kuka kasance kunã ƙaryatãwa game da ita."
Verse 15
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
"To, shin wannan sihiri ne kõ kuwa kũ ne bã ku gani?"
Verse 16
"Ku shigẽ ta. To, ku yi haƙuri ko kuma kada ku yi haƙuri, dai dai ne a kanku, kawai anã yi muku sakamakon abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
Verse 17
ﭦﭧﭨﭩﭪ
ﭫ
Lalle, mãsu taƙawa, sunã a cikin gidãjen Aljanna da wata ni'ima.
Verse 18
Sunã mãsu jin dãɗi da abin da Ubangijinsu Ya ba su, kuma Ubangijinsu Ya tsãre musu azãbar Jahĩm.
Verse 19
ﭵﭶﭷﭸﭹﭺ
ﭻ
(A ce musu): "Ku ci, ku sha, da ni'ima, dõmin abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
Verse 20
Sunã kishingiɗe a kan karagu waɗanda ke cikin sahu, kuma Muka aurar da su waɗansu mãtã mãsu farin idãnu, mãsu girmansu.
Verse 21
Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma zũriyarsu suka bĩ su ga ĩmãnin, Mun riskar da zũriyarsu da su, alhãli kuwa bã da Mun rage musu kõme ba daga aikinsu, kõwane mutum jingina ne ga abin da ya sana'anta.
Verse 22
ﮚﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Kuma Muka yalwata musu 'ya'yan itãce da nãma irin wanda suke marmari.
Verse 23
Sunã mĩƙa wa jũnansu a cikinta hinjãlan giya, wadda bãbu yãsassar magana a cikinta, kuma bãbu jin nauyin zunubi.
Verse 24
Kuma waɗansu samãri nã gẽwayãwa a kansu, kamar dai sũ lu'ulu'u ne wanda ke kulle.
Verse 25
ﯓﯔﯕﯖﯗ
ﯘ
Waɗansunsu suka fuskanta zuwa ga waɗansu, sunã tambayar jũna.
Verse 26
Suka ce: "Lalle mũ mun kasance a gabãnin wannan (a dũniya) a cikin iyãlanmu munã jin tsõro."
Verse 27
ﯡﯢﯣﯤﯥﯦ
ﯧ
"To, Allah Yã yi mana kyautar falala, kuma Yã tsare mana azãbar iskar zãfi."
Verse 28
"Lalle mũ mun kasance, a gãbanin haka, munã kiran sa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai kyautatãwa, Mai rahama."
Verse 29
To, ka tunãtar kai fa sabõda ni'imar Ubangjinka, bã bõka kake ba, kuma bã mahaukaci ba.
Verse 30
Shin zã su ce: "Mawãƙi ne, munã jiran, masĩfun mutuwa game da shĩ"?
Verse 31
ﰄﰅﰆﰇﰈﰉ
ﰊ
Ka ce: "Ku yi jira, domin nĩ ma lalle inã a cikin mãsu jira tãre da ku."
Verse 32
Shin, hankulansu ne ke umarin su da wannan, kõ kuwa sũ wasu mutãne ne mãsu ƙetare haddi?
Verse 33
Shin, cẽwa suke yi: "Shi ne ke ƙãga faɗarsa"? Ã'a ba su dai yi ĩmãni ba.
Verse 34
ﭣﭤﭥﭦﭧﭨ
ﭩ
Sai su zõ da wani lãbãri mai misãlinsa idan sun kasance sũmãsu gaskiya ne.
Verse 35
Shin, an halitta su ne bã daga kõme ba, kõ kuwa sũ ne mãsu yin halitta?
Verse 36
Shin, sun halitta sammai da ƙasa ne? Ã'a ba su dai yi ĩmãnin yaƙĩni ba.
Verse 37
Shin, taskõkin Ubangijinka, sunã a wurinsu ne? Kõ kuwa sũ ne mãsu rinjãya?
Verse 38
Shin, sunã da wani tsãni ne wanda suke (hawa sunã) saurãron (lãbãrin samã) a cikinsa? Sai mai saurarõnsu ya zo da wani dalĩli bayyananne.
Verse 39
ﮏﮐﮑﮒﮓ
ﮔ
Shin, Yanã da 'ya'ya mãtã ne kuma kũ, kunã da ɗiya maza ne?
Verse 40
Shin, kanã tambayar su wata ijãra ne, sabõda haka suka zama mãsu jin nauyin biyan tãrar?
Verse 41
ﮝﮞﮟﮠﮡ
ﮢ
Shin, a wurinsu akwai ilmin gaibi, sabõda haka sunã rubũtãwa?
Verse 42
Shin, sunã nufin wani kaidi ne? To, waɗanda suka kãfirta sũ ne waɗanda ake yi wa kaidi.
Verse 43
Shin, sunã da wani abin bautãwa ne wanda bã Allah ba? Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke yi na shirki!
Verse 44
Kuma idan sun ga wani ɓaɓɓake daga samã yãnã fãɗuwa, sai su ce wani girgije ne, mai hauhawar jũna.
Verse 45
To, ka bar su, sai sun haɗu da yinin nan da za a sũmar da su a cikinsa.
Verse 46
Rãnar da kaidinsu bã ya wadãtar masu da kõme, kuma bã a taimakon su.
Verse 47
Kuma lalle, waɗannan da suka yi zãluncin, sunã da azãba (a nan dũniya) banda waccan, kuma mafi yawansu ba su sani ba.
Verse 48
Sai ka yi hakuri da hukuncin Ubangijinka, lalle kai fa kanã idãnunMu, kuma ka tsarkake Ubangijinka da (tasbĩhi) game da gõde Masa a lõkacin da kake tãshi tsaye (dõmin salla kõ wani abu).
Verse 49
ﰋﰌﰍﰎﰏ
ﰐ
Kuma daga dare, sai ka tsarkake Shi (da tasbĩhin) dalõkacin jũyãwar taurãri.
تقدم القراءة