سورة النازعات

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Fassarar Surar An-Nazi'at a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Verse 1

An-Nazi'at


Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
Verse 2

Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
Verse 3

Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
Verse 4

Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
Verse 5

Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
Verse 6

Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
Verse 7

Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
Verse 8

Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
Verse 9

Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
Verse 19

"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
Verse 21

Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
Verse 22

Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
Verse 23

Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.

Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
Verse 28

Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
Verse 33

Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
Verse 38

Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
Verse 44

Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
تقدم القراءة