سورة الشعراء

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Fassarar Surar As-Shu'ara a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Verse 1

As-Shu'ara


¦. S̃. M̃.

(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!

Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."

Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."
Verse 46

Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.
Verse 55

"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."
Verse 56

"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."
Verse 60

Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.

Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."

Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.
Verse 66

Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.

Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.

Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."
Verse 79

"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."
Verse 90

Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.
Verse 91

Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.
Verse 108

"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Verse 110

"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"

Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"

"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."

Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.
Verse 122

Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.
Verse 125

"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."
Verse 126

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Verse 128

"Shin, kunã yin ginin sitadiyo a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"
Verse 129

"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?"
Verse 130

"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."
Verse 131

"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Verse 133

"Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya."
Verse 138

"Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."
Verse 140

Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Verse 144

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã.
Verse 148

"Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi mãsu narkẽwa a ciki?"
Verse 150

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Verse 157

Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.
Verse 163

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."
Verse 169

"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."
Verse 170

Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.
Verse 175

Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Verse 179

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã."
Verse 184

"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko."
Verse 192

Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.
Verse 196

Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.
Verse 204

Ashe, to, da azãbarMu suke nẽman gaggãwa?
Verse 205

Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru,
Verse 206

Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,

Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare su.
Verse 210

Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.
Verse 211

Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.
Verse 212

Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.

Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.
Verse 214

Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci.

Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."
Verse 223

Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.

Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba?
تقدم القراءة