Fassarar Surar Al-Fajr a الهوساوية daga Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
Verse 1
ﭤ
ﭥ
Al-Fajr
Inã rantsuwa da alfijiri.
Verse 2
ﭦﭧ
ﭨ
Da darũruwa gõma.
Verse 3
ﭩﭪ
ﭫ
Da (adadi na) cikã da (na) mãrã.
Verse 4
ﭬﭭﭮ
ﭯ
Da dare idan yana shũɗewa.
Verse 5
ﭰﭱﭲﭳﭴﭵ
ﭶ
Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?
Verse 6
ﭷﭸﭹﭺﭻﭼ
ﭽ
Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba?
Verse 7
ﭾﭿﮀ
ﮁ
Iramawa mãsu sakon ƙĩrar jiki.
Verse 8
ﮂﮃﮄﮅﮆﮇ
ﮈ
Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).
Verse 9
ﮉﮊﮋﮌﮍ
ﮎ
Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi suka yi gidãje)?
Verse 10
ﮏﮐﮑ
ﮒ
Da Fir'auna mai turãku.
Verse 11
ﮓﮔﮕﮖ
ﮗ
Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa?
Verse 12
ﮘﮙﮚ
ﮛ
Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu.
Verse 13
ﮜﮝﮞﮟﮠ
ﮡ
Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.
Verse 14
ﮢﮣﮤ
ﮥ
Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.
Verse 15
To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."
Verse 16
Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."
Verse 17
ﯞﯟﯠﯡﯢﯣ
ﯤ
A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya!
Verse 18
ﯥﯦﯧﯨﯩ
ﯪ
Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!
Verse 19
ﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa.
Verse 20
ﯰﯱﯲﯳ
ﯴ
Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa.
Verse 21
A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai.
Verse 22
ﯽﯾﯿﰀﰁ
ﰂ
Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, safũ- safu.
Verse 23
Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!
Verse 24
ﭜﭝﭞﭟ
ﭠ
Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!"
Verse 25
ﭡﭢﭣﭤﭥ
ﭦ
To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah.
Verse 26
ﭧﭨﭩﭪ
ﭫ
Kuma bãbu wani mai ɗauri irin ɗaurinSa.
Verse 27
ﭬﭭﭮ
ﭯ
Yã kai rai mai natsuwa!
Verse 28
ﭰﭱﭲﭳﭴ
ﭵ
Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhãli kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a dũniya) abar yardarwa (da sakamakon da zã a ba ka a Lãhira).
Verse 29
ﭶﭷﭸ
ﭹ
Sabõbda haka, ka shiga cikin bãyiNa (mãsu bin umurui a dũniya).
Verse 30
ﭺﭻ
ﭼ
Kuma ka shiga AljannaTa (a Lãhira).
تقدم القراءة