سورة نوح

الترجمة الهوساوية

ترجمة معاني سورة نوح باللغة الهوساوية من كتاب الترجمة الهوساوية

الترجمة الهوساوية

الناشر

مجمع الملك فهد

آية رقم 6
"To, amma kirana bai ƙãre su ba sai da, gudu (daga gare ni)."
"Kuma lalle ne ni, kõ da yaushe na kirãye su dõmin Ka gãfarta musu, sai su sanya yatsunsu a cikin kunnuwansu, su lulluɓe da tufãfinsu, su dõge ga yin laifi. Sun yi girman kai iyãkar girman kai."
آية رقم 10
"Shi na ce, 'Ku nẽmi gãfara daga Ubangijinku, lalle ne shi Ya kasance Mai gãfara ne."
آية رقم 11
"Ya sako (girgijen) sama a kanku da ruwa mai ɓuɓɓuga."
"Kuma ya yalwata muku game da dũkiya da ɗiya, Ya sanya muku (albarka) ga gõnaki, kuma Ya sanya muku koguna."
آية رقم 14
"Alhãli kuwa, lalle ne, Ya halitta. ku, a cikin hãlãye?"
آية رقم 17
"Kuma Allah Ya tsirar da ku daga ƙasa (kamar ganye) tsirarwa."
آية رقم 18
"Sa'an nan Ya mayar da ku a cikinta, kuma Ya fitar da ku fitarwa."
آية رقم 20
"Dõmin ku shiga a cikinta, hanyõyi mãsu fãɗi."
آية رقم 22
"Kuma sun yi wani mãkirci, mãkirci babba."
"Ya Ubanginjina! Ka yi mini gãfara (ni) da mahaifana biyu, da wanda ya shiga gidana, yana mai ĩmãni, da mũminai maza da mũminai mãtã, kuma kada Ka ƙãrã wa azzãlumai kõme sai halaka."
تقدم القراءة