سورة النجم

الترجمة الهوساوية

ترجمة معاني سورة النجم باللغة الهوساوية من كتاب الترجمة الهوساوية

الترجمة الهوساوية

الناشر

مجمع الملك فهد

آية رقم 1
Inã rantsuwa da taurãron, a lõkacin da ya faku.
آية رقم 5
(Malã'ika) mai tsananin ƙarfi *ya sanar da shi.
* Wahayin da ke zuwa ga Annabi bãbu ɓata a cikinsa dõmin Jibrilu mai kãwo shi ga Annabi, Malã'ika ne mai ƙarfi ƙwarai, wani Shaiɗãni bã ya iya taron sa dõmin ya musanya wahayin, kuma Annabi ya san shi sõsai, kuma idan ya kãwo wahayin, sai ya sauko kusa ƙwarai da Annabi, sa'an nan shi kuma Annabi ba rikitacce ba ne, yanã cikin hankalinsa.
آية رقم 6
Ma'abũcin ƙarfi da kwarjini, sa'an nan ya daidaita.
آية رقم 7
Alhãli kuwa yanã a sararin samã mafi aukaka.
آية رقم 8
Sa'an nan ya kusanta, kuma ya matsa zurõwa.
آية رقم 9
Har ya kasance gwargwadon zirã'i biyu, kõ kuma abin da ya fi kusa.
آية رقم 10
Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bãwan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa).
آية رقم 12
Shin, zã ku yi masa musu a kan abin da yake gani?
آية رقم 13
Kuma lalle ya gan shi, haƙĩƙatan, a wani lõkacin saukarsa.*
* Lamirin Malã'ika Jibrila ne.
آية رقم 15
A inda taken, nan Aljannar makoma take.
آية رقم 17
Ganinsa* bai karkata ba, kuma bai ƙetare haddi ba.
* Lamirin Malã'ika Jibrila ne.
آية رقم 18
Lalle, tabbas, (Annabinku) ya ga waɗanda suka fi girma* daga ãyõyin Ubangijinsa.
 * Watau dai Alƙur'ani ya zo daga Allah ta hanya mafi aminci har ya sadu da mutãne dõmin su yi aiki da abin da ke cikinsa.
آية رقم 19
Shin, kun ga Lãta da uzza?(5)
 (5) Watau kun bar Alƙur'ani kun kõma wa surkullen da kuke haɗãwa game da gumãka su Lãta da Uzza da Manãta. Kuna cewa sũ wakĩlan Mala'ikun da kuke bautã wa ne kuma su 'ya'yan Allah mãtã ne. Sunã cetonku daga Allah.
آية رقم 20
Da (wani gunki wai shi) Manãta, na ukunsu?
آية رقم 21
Ashe, kũ ne da ɗa namiji Shĩ (Allah) kuma da ɗiya mace?
Waɗannan bã kõme ba ne fãce sũnãye, waɗanda kuka ambace su da su, kũ da uwãyenku. Allah bai saukar da wani dalĩli game da su ba. (Kãfirai) bã su biyar kõme fãce zato da abin da rãyukansu ke so, Alhãli kuwa shiriyar(6) ta daga wajen Ubangijinsu, ta jẽ musu (sai suka bar ta suka kõma wa zaton).
(6) Watau Alƙur'ani wanda Mala'ika jibrĩla ya zo wa Annabi da shi. Sun bar shi sun kõma wa tatsũniyõyi da gũrace-gũrace.
آية رقم 24
Ko (an fai cẽwa) mutum zai sãmi abin da yake gũri?
آية رقم 25
To, Lãhira da dũniya na Allah kawai ne (wanda ya nẽme su daga wani, yã yi kuskure).
Kuma abin da ke cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasã na Allah kawai ne, dõmin Yã sãka wa waɗanda suka mũnana da abin da suka aikata, kuma Ya sãka wa waɗanda suki kyautata da sakamakon da ya fi kyau.
Waɗanda ke nĩsantar manyan zunubai da abũbuwan alfãsha, fãce ƙanãnan laifuffuka, lalle Ubangijinka Mai yalwatattar gãfara ne, Shĩ ne Ya fi sani ga abinda ke gare ku a lõkacin da Ya ƙãga halittarku daga ƙasa, kuma a lõkacin da kuke tãyuna a cikin cikannan uwãyenku. Sabõda haka, kada ku tsarkake* kanku, Shĩ ne Mafi sani ga wanda ya yi taƙawa.
  * Wanda yake mutumin kirki, Allah Ya san shi. Kada ku dinga tsarkake kanku da bãkunanku dõmin neman girma, kõ dõmin neman wani abu dabam.
آية رقم 35
Shin, akwai ilmin gaibi a wurinsa, Sabõda haka yanã ganin gaibin?
آية رقم 38
Cẽwa wani rai mai kãyan laifi bã ya ɗaukar kãyan laifin wani.
آية رقم 41
Sa'an nan a sãka masa da sakamako wanda yake mafi cikar ma'auni?
آية رقم 43
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya sanya dariya, kuma Ya sanya kũka.
آية رقم 44
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya kashe, kuma Ya rãyar.
آية رقم 46
Daga wani ɗigon ruwa guda a lõkacin da ake jẽfa shi a cikin mahaifa.
آية رقم 48
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya azurta, kuma Ya wadãtar.
آية رقم 49
Kuma lalle, Shĩ, Shi ne Ubangijin Shi'ira.*
* Sũnan wasu taurãri biyu ne sunã fita a bãyan taurarin Jauza'a sunã tafiya daga kudu zuwa arewa karkace. Kabĩlar Lãrabãwa ta Khuza'a na bauta musu da umurnin Abu Kabshah, ɗaya daga cikin kãkannin Annabi na wajen uwa dõmin haka ne Ƙuraishãwa ke ce wa Annabi Ibn abĩ Kabshah, wanda ya ƙãga sãbon addinĩn da ya sãɓawa na ubanninsa.
آية رقم 50
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya halaka Ãdãwa na farko.
آية رقم 51
Da Samũdãwa, sa'an nan bai rage su ba.
آية رقم 53
Da waɗanda aka birkice *ƙasarsu, Ya kãyar da su.
 * Mutãnen Lũɗu da aka birkice ƙasarsu da su.
آية رقم 54
Sa'an nan abin da ya rufe su, ya rufe su.
آية رقم 55
To, da wace daga ni'imõmin Ubangijinka kake *yin shakka?
* Kamar abõkin magana kõ mai karãtu.
آية رقم 56
wannan (Muhammadu) mai gargaɗi ne kamar irin mãsu gargaɗi na farko.
آية رقم 57
Makusanciya* fa, tã yi kusa.
 * Makusanciya ita ce Ƙiyãma.
آية رقم 59
Shin, kuma daga wannan (5)lãbãri kuke mãmãki?
 (5) Al'ƙur'ãni.
آية رقم 60
Kuma kunã yin dãriya, kuma bã ku yin kũka?
آية رقم 61
Alhãli kunã mãsu wãsã?
آية رقم 62
To, ku yi tawãli'u (6)ga Allah, kuma ku bauta (masa).
 (6) Anã yin sujadar karatu a nan, amma bã ta a cikin sujadai na tĩlas.
تقدم القراءة