ترجمة معاني سورة النجم باللغة الهوساوية من كتاب الترجمة الهوساوية
آية رقم 1
ﭑﭒﭓ
ﭔ
Inã rantsuwa da taurãron, a lõkacin da ya faku.
آية رقم 2
ﭕﭖﭗﭘﭙ
ﭚ
Ma'abũcinku bai ɓata ba, kuma bai ƙẽtare haddi ba.
آية رقم 3
ﭛﭜﭝﭞ
ﭟ
Kuma bã ya yin magana daga son zuciyarsa.
آية رقم 4
ﭠﭡﭢﭣﭤ
ﭥ
(Maganarsa) ba ta zamo ba, fãce wahayi ne da ake aikõwa.
آية رقم 5
ﭦﭧﭨ
ﭩ
(Malã'ika) mai tsananin ƙarfi *ya sanar da shi.
* Wahayin da ke zuwa ga Annabi bãbu ɓata a cikinsa dõmin Jibrilu mai kãwo shi ga Annabi, Malã'ika ne mai ƙarfi ƙwarai, wani Shaiɗãni bã ya iya taron sa dõmin ya musanya wahayin, kuma Annabi ya san shi sõsai, kuma idan ya kãwo wahayin, sai ya sauko kusa ƙwarai da Annabi, sa'an nan shi kuma Annabi ba rikitacce ba ne, yanã cikin hankalinsa.
آية رقم 6
ﭪﭫﭬ
ﭭ
Ma'abũcin ƙarfi da kwarjini, sa'an nan ya daidaita.
آية رقم 7
ﭮﭯﭰ
ﭱ
Alhãli kuwa yanã a sararin samã mafi aukaka.
آية رقم 8
ﭲﭳﭴ
ﭵ
Sa'an nan ya kusanta, kuma ya matsa zurõwa.
آية رقم 9
ﭶﭷﭸﭹﭺ
ﭻ
Har ya kasance gwargwadon zirã'i biyu, kõ kuma abin da ya fi kusa.
آية رقم 10
ﭼﭽﭾﭿﮀ
ﮁ
Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bãwan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa).
آية رقم 11
ﮂﮃﮄﮅﮆ
ﮇ
Zũciyar (Annabi) bata ƙaryata abin da ya gani ba.
آية رقم 12
ﮈﮉﮊﮋ
ﮌ
Shin, zã ku yi masa musu a kan abin da yake gani?
آية رقم 13
ﮍﮎﮏﮐ
ﮑ
Kuma lalle ya gan shi, haƙĩƙatan, a wani lõkacin saukarsa.*
* Lamirin Malã'ika Jibrila ne.
آية رقم 14
ﮒﮓﮔ
ﮕ
A wurin da magaryar tuƙẽwa take.
آية رقم 15
ﮖﮗﮘ
ﮙ
A inda taken, nan Aljannar makoma take.
آية رقم 16
ﮚﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Lõkacin da abin da yake rufe magaryar tuƙẽwa ya rufe ta.
آية رقم 17
ﮠﮡﮢﮣﮤ
ﮥ
Ganinsa* bai karkata ba, kuma bai ƙetare haddi ba.
* Lamirin Malã'ika Jibrila ne.
آية رقم 18
ﮦﮧﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
Lalle, tabbas, (Annabinku) ya ga waɗanda suka fi girma* daga ãyõyin Ubangijinsa.
* Watau dai Alƙur'ani ya zo daga Allah ta hanya mafi aminci har ya sadu da mutãne dõmin su yi aiki da abin da ke cikinsa.
آية رقم 19
ﮭﮮﮯ
ﮰ
Shin, kun ga Lãta da uzza?(5)
(5) Watau kun bar Alƙur'ani kun kõma wa surkullen da kuke haɗãwa game da gumãka su Lãta da Uzza da Manãta. Kuna cewa sũ wakĩlan Mala'ikun da kuke bautã wa ne kuma su 'ya'yan Allah mãtã ne. Sunã cetonku daga Allah.
آية رقم 20
ﮱﯓﯔ
ﯕ
Da (wani gunki wai shi) Manãta, na ukunsu?
آية رقم 21
ﯖﯗﯘﯙ
ﯚ
Ashe, kũ ne da ɗa namiji Shĩ (Allah) kuma da ɗiya mace?
آية رقم 22
ﯛﯜﯝﯞ
ﯟ
Wannan fa ya zama rabo naƙasasshe.
آية رقم 23
Waɗannan bã kõme ba ne fãce sũnãye, waɗanda kuka ambace su da su, kũ da uwãyenku. Allah bai saukar da wani dalĩli game da su ba. (Kãfirai) bã su biyar kõme fãce zato da abin da rãyukansu ke so, Alhãli kuwa shiriyar(6) ta daga wajen Ubangijinsu, ta jẽ musu (sai suka bar ta suka kõma wa zaton).
(6) Watau Alƙur'ani wanda Mala'ika jibrĩla ya zo wa Annabi da shi. Sun bar shi sun kõma wa tatsũniyõyi da gũrace-gũrace.
آية رقم 24
ﯼﯽﯾﯿ
ﰀ
Ko (an fai cẽwa) mutum zai sãmi abin da yake gũri?
آية رقم 25
ﰁﰂﰃ
ﰄ
To, Lãhira da dũniya na Allah kawai ne (wanda ya nẽme su daga wani, yã yi kuskure).
آية رقم 26
Akwai malã'iku da yawa a cikin sammai cẽtonsu bã ya wadãtar da kõme fãce bãyan Allah Yã yi izni (da shi) ga wanda Yake so, kuma Yake yarda.
آية رقم 27
Lalle waɗannan da bã su yin ĩmãni da Lãhira, haƙĩƙa sunã kiran malã'iku da sũnan mace.
آية رقم 28
Kuma bã su da wani ilmi game da shi, bã su bin kõme fãce zato alhãli kuwa lalle zato bã ya amfãnar da kõme daga gaskiya.
آية رقم 29
Sabõda haka sai ka kau da kai daga wanda ya jũya bãya daga ambatonMu kuma bai yi nufin kõme ba fãce rãyuwar kusa (dũniya).
آية رقم 30
Wannan ita ce iyãkar abin da suke iya kai gare shi na ilmi. lalle Ubangijinka Shĩ ne Mafi sanin wanda ya ɓace daga hanyarSa, kuma Shi ne Mafi sani ga wanda ya nẽmi shiriya.
آية رقم 31
Kuma abin da ke cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasã na Allah kawai ne, dõmin Yã sãka wa waɗanda suka mũnana da abin da suka aikata, kuma Ya sãka wa waɗanda suki kyautata da sakamakon da ya fi kyau.
آية رقم 32
Waɗanda ke nĩsantar manyan zunubai da abũbuwan alfãsha, fãce ƙanãnan laifuffuka, lalle Ubangijinka Mai yalwatattar gãfara ne, Shĩ ne Ya fi sani ga abinda ke gare ku a lõkacin da Ya ƙãga halittarku daga ƙasa, kuma a lõkacin da kuke tãyuna a cikin cikannan uwãyenku. Sabõda haka, kada ku tsarkake* kanku, Shĩ ne Mafi sani ga wanda ya yi taƙawa.
* Wanda yake mutumin kirki, Allah Ya san shi. Kada ku dinga tsarkake kanku da bãkunanku dõmin neman girma, kõ dõmin neman wani abu dabam.
آية رقم 33
ﯢﯣﯤ
ﯥ
Shin, ka ga wannan da ya jũya baya?
آية رقم 34
ﯦﯧﯨ
ﯩ
Ya yi kyauta kaɗan, kuma ya yi rowa?
آية رقم 35
ﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
Shin, akwai ilmin gaibi a wurinsa, Sabõda haka yanã ganin gaibin?
آية رقم 36
Ko kuwa ba a ba shi lãbãri ba ga abin da yake a cikin Littafan Mũsã?
آية رقم 37
ﯸﯹﯺ
ﯻ
Da Ibrãhĩm wanda ya cika alkawari?
آية رقم 38
ﯼﯽﯾﯿﰀ
ﰁ
Cẽwa wani rai mai kãyan laifi bã ya ɗaukar kãyan laifin wani.
آية رقم 39
ﰂﰃﰄﰅﰆﰇ
ﰈ
Kuma mutum bã shi da kõme fãce abin da ya aikata.
آية رقم 40
ﰉﰊﰋﰌ
ﰍ
Kuma lalle, aikinsa zã a gan shi.
آية رقم 41
ﰎﰏﰐﰑ
ﰒ
Sa'an nan a sãka masa da sakamako wanda yake mafi cikar ma'auni?
آية رقم 42
ﰓﰔﰕﰖ
ﰗ
Kuma lalle, makõmar zuwa Ubangijinka kawai take?
آية رقم 43
ﰘﰙﰚﰛ
ﰜ
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya sanya dariya, kuma Ya sanya kũka.
آية رقم 44
ﰝﰞﰟﰠ
ﰡ
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya kashe, kuma Ya rãyar.
آية رقم 45
ﭑﭒﭓﭔﭕ
ﭖ
Kuma lalle Shĩ ne Ya yi halitta nau'i-nau'i, namiji da mace.
آية رقم 46
ﭗﭘﭙﭚ
ﭛ
Daga wani ɗigon ruwa guda a lõkacin da ake jẽfa shi a cikin mahaifa.
آية رقم 47
ﭜﭝﭞﭟ
ﭠ
Kuma a kansa ne ƙãga halitta ta biyu take.
آية رقم 48
ﭡﭢﭣﭤ
ﭥ
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya azurta, kuma Ya wadãtar.
آية رقم 49
ﭦﭧﭨﭩ
ﭪ
Kuma lalle, Shĩ, Shi ne Ubangijin Shi'ira.*
* Sũnan wasu taurãri biyu ne sunã fita a bãyan taurarin Jauza'a sunã tafiya daga kudu zuwa arewa karkace. Kabĩlar Lãrabãwa ta Khuza'a na bauta musu da umurnin Abu Kabshah, ɗaya daga cikin kãkannin Annabi na wajen uwa dõmin haka ne Ƙuraishãwa ke ce wa Annabi Ibn abĩ Kabshah, wanda ya ƙãga sãbon addinĩn da ya sãɓawa na ubanninsa.
آية رقم 50
ﭫﭬﭭﭮ
ﭯ
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya halaka Ãdãwa na farko.
آية رقم 51
ﭰﭱﭲ
ﭳ
Da Samũdãwa, sa'an nan bai rage su ba.
آية رقم 52
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sũ sun kasance mafi zãlunci kuma mafi girman kai.
آية رقم 53
ﭿﮀ
ﮁ
Da waɗanda aka birkice *ƙasarsu, Ya kãyar da su.
* Mutãnen Lũɗu da aka birkice ƙasarsu da su.
آية رقم 54
ﮂﮃﮄ
ﮅ
Sa'an nan abin da ya rufe su, ya rufe su.
آية رقم 55
ﮆﮇﮈﮉ
ﮊ
To, da wace daga ni'imõmin Ubangijinka kake *yin shakka?
* Kamar abõkin magana kõ mai karãtu.
آية رقم 56
ﮋﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
wannan (Muhammadu) mai gargaɗi ne kamar irin mãsu gargaɗi na farko.
آية رقم 57
ﮑﮒ
ﮓ
Makusanciya* fa, tã yi kusa.
* Makusanciya ita ce Ƙiyãma.
آية رقم 58
ﮔﮕﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
Bãbu wani rai, banda Allah, mai iya bãyani gare ta.
آية رقم 59
ﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Shin, kuma daga wannan (5)lãbãri kuke mãmãki?
(5) Al'ƙur'ãni.
آية رقم 60
ﮠﮡﮢ
ﮣ
Kuma kunã yin dãriya, kuma bã ku yin kũka?
آية رقم 61
ﮤﮥ
ﮦ
Alhãli kunã mãsu wãsã?
آية رقم 62
ﮧﮨﮩﮪ
ﮫ
To, ku yi tawãli'u (6)ga Allah, kuma ku bauta (masa).
(6) Anã yin sujadar karatu a nan, amma bã ta a cikin sujadai na tĩlas.
تقدم القراءة