ترجمة معاني سورة التكوير باللغة الهوساوية من كتاب الترجمة الهوساوية
آية رقم 1
ﭙﭚﭛ
ﭜ
Idan rãna aka shafe haskenta
آية رقم 2
ﭝﭞﭟ
ﭠ
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).
آية رقم 3
ﭡﭢﭣ
ﭤ
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.
آية رقم 4
ﭥﭦﭧ
ﭨ
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna* aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
* Rãƙuma mãsu ciki ɗan wata gõma.
آية رقم 5
ﭩﭪﭫ
ﭬ
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.
آية رقم 6
ﭭﭮﭯ
ﭰ
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.
آية رقم 7
ﭱﭲﭳ
ﭴ
Kuma idan rãyuka aka haɗa* su da jikunkunansu.
* Ko kuma, aka haɗa kõwane mutum da irin mutãnensa a Aljanna ko a wuta.
آية رقم 8
ﭵﭶﭷ
ﭸ
Kuma idan wadda aka turbuɗe* ta da rai aka tambaye ta.
* A cikin zãmanin jahiliyya Lãrabãwa bã su son a haifa musu 'ya'ya mãta dõmin haka har sukan turbuɗe 'ya'yansu dõmin kada su yi abin kunya ko kuma su talauce wajen yi musu aure.
آية رقم 9
ﭹﭺﭻ
ﭼ
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"
آية رقم 10
ﭽﭾﭿ
ﮀ
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).
آية رقم 11
ﮁﮂﮃ
ﮄ
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.
آية رقم 12
ﮅﮆﮇ
ﮈ
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta
آية رقم 13
ﮉﮊﮋ
ﮌ
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.
آية رقم 14
ﮍﮎﮏﮐ
ﮑ
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).
آية رقم 15
ﮒﮓﮔ
ﮕ
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã* ba.
* Masu tafiya suna kõmawa bãya.
آية رقم 16
ﮖﮗ
ﮘ
Mãsu gudu suna ɓũya.
آية رقم 17
ﮙﮚﮛ
ﮜ
Da dare idan ya bãyar da bãya.
آية رقم 18
ﮝﮞﮟ
ﮠ
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.
آية رقم 19
ﮡﮢﮣﮤ
ﮥ
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.
آية رقم 20
ﮦﮧﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.
آية رقم 21
ﮭﮮﮯ
ﮰ
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.
آية رقم 22
ﮱﯓﯔ
ﯕ
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.
آية رقم 23
ﯖﯗﯘﯙ
ﯚ
Kuma lalle ne, yã gan shi(5) a cikin sararin sama mabayyani.
(5) Annabi ya ga Mala'ika Jibirilu ya san shi. Sabõda haka wani aljani bã zai yi kama da shi ba balle ya kãwo masa ƙarya.
آية رقم 24
ﯛﯜﯝﯞﯟ
ﯠ
Kuma shi, ga gaibi(6) bã mai rowa ba ne.
(6) Ma'anar gaibi a nan, ilmin da Allah Ya aiko Jibirilu da shi zuwa ga Annabi Annabi ba ya ɓõye shi daga mutãne. Ga wata ƙira'a, wanda ake tuhuma, wãto ba a tuhumar Annabi, ga gaibin da ya faɗi cewa daga Allah yake, wato Alƙur'ãni duka gaskiya ne.
آية رقم 25
ﯡﯢﯣﯤﯥ
ﯦ
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.
آية رقم 26
ﯧﯨ
ﯩ
Shin, a inã zã ku tafi?
آية رقم 27
ﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.
آية رقم 28
ﯰﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.
آية رقم 29
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.
تقدم القراءة