سورة القيامة

الترجمة الهوساوية

ترجمة معاني سورة القيامة باللغة الهوساوية من كتاب الترجمة الهوساوية

الترجمة الهوساوية

الناشر

مجمع الملك فهد

آية رقم 1
Bã sai Nã yi rantsuwa* da Rãnar ¡iyãma ba.
* Wasu na fassarawa: lna rantsuwa da Rãnar Ƙiyama. A ganina, da tabbatar da rantsuwar da kuma kore ta duka ɗaya ne, maƙasũdi dai jan hankalin mai karãtu ga abin da yake a ciki, na hikimar Allah.
آية رقم 2
Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin* kansa ba.
* Kowane rai na zargin kansa idan bai yi aikin alheri ba, ko kuma bai yi fiye da wanda ya yi ba, ko kuma bai aikata wanda ya fi kyãwo ba a lokacin aikinsa.
آية رقم 5
Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.
آية رقم 7
To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).
آية رقم 8
Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).
آية رقم 12
zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.
آية رقم 13
Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.
آية رقم 15
Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).
آية رقم 16
Kada ka mõtsar* da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).
 * Dangantakar wannan ãya da ta sama da ita, ita ce bambancin Annabi mai gaggawar karɓar umurnin Allah da ƙyamar kãfiri ga karɓarsa, da bayãnin sauƙaƙewar Allah ga mai bin umurninSa.
آية رقم 17
Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.
آية رقم 19
sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.
آية رقم 20
A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.
آية رقم 21
Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).
آية رقم 22
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.
آية رقم 24
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.
آية رقم 29
Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.
آية رقم 30
Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa* take.
 * Ranar kora mutane, kamar ana gargaɗa tumãki, zuwa ga tsayuwa a gaba ga Allah, dõmin hisabi.
آية رقم 32
Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!
آية رقم 34
Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.
آية رقم 35
Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.
آية رقم 36
Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?
آية رقم 38
Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;
آية رقم 40
Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?*
 * Ana son mai karãtu a nan ya ce: a ɓoye بلى وأنا على ذلك من الشاهدين.
تقدم القراءة