ترجمة معاني سورة القيامة باللغة الهوساوية من كتاب الترجمة الهوساوية
آية رقم 1
ﮊﮋﮌﮍ
ﮎ
Bã sai Nã yi rantsuwa* da Rãnar ¡iyãma ba.
* Wasu na fassarawa: lna rantsuwa da Rãnar Ƙiyama. A ganina, da tabbatar da rantsuwar da kuma kore ta duka ɗaya ne, maƙasũdi dai jan hankalin mai karãtu ga abin da yake a ciki, na hikimar Allah.
آية رقم 2
ﮏﮐﮑﮒ
ﮓ
Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin* kansa ba.
* Kowane rai na zargin kansa idan bai yi aikin alheri ba, ko kuma bai yi fiye da wanda ya yi ba, ko kuma bai aikata wanda ya fi kyãwo ba a lokacin aikinsa.
آية رقم 3
ﮔﮕﮖﮗﮘ
ﮙ
Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?
آية رقم 4
ﮚﮛﮜﮝﮞﮟ
ﮠ
Na'am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.
آية رقم 5
ﮡﮢﮣﮤﮥ
ﮦ
Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.
آية رقم 6
ﮧﮨﮩﮪ
ﮫ
Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"
آية رقم 7
ﮬﮭﮮ
ﮯ
To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).
آية رقم 8
ﮰﮱ
ﯓ
Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).
آية رقم 9
ﯔﯕﯖ
ﯗ
Aka tãra rãnã da watã
آية رقم 10
ﯘﯙﯚﯛﯜ
ﯝ
Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"
آية رقم 11
ﯞﯟﯠ
ﯡ
A'aha! bãbu mafaka.
آية رقم 12
ﯢﯣﯤﯥ
ﯦ
zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.
آية رقم 13
ﯧﯨﯩﯪﯫﯬ
ﯭ
Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.
آية رقم 14
ﯮﯯﯰﯱﯲ
ﯳ
Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.
آية رقم 15
ﯴﯵﯶ
ﯷ
Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).
آية رقم 16
ﯸﯹﯺﯻﯼﯽ
ﯾ
Kada ka mõtsar* da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).
* Dangantakar wannan ãya da ta sama da ita, ita ce bambancin Annabi mai gaggawar karɓar umurnin Allah da ƙyamar kãfiri ga karɓarsa, da bayãnin sauƙaƙewar Allah ga mai bin umurninSa.
آية رقم 17
ﯿﰀﰁﰂ
ﰃ
Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.
آية رقم 18
ﰄﰅﰆﰇ
ﰈ
To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.
آية رقم 19
ﰉﰊﰋﰌ
ﰍ
sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.
آية رقم 20
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.
آية رقم 21
ﭖﭗ
ﭘ
Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).
آية رقم 22
ﭙﭚﭛ
ﭜ
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.
آية رقم 23
ﭝﭞﭟ
ﭠ
Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne.
آية رقم 24
ﭡﭢﭣ
ﭤ
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.
آية رقم 25
ﭥﭦﭧﭨﭩ
ﭪ
Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso.
آية رقم 26
ﭫﭬﭭﭮ
ﭯ
A'aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai.
آية رقم 27
ﭰﭱﭲﭳ
ﭴ
kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"
آية رقم 28
ﭵﭶﭷ
ﭸ
Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce.
آية رقم 29
ﭹﭺﭻ
ﭼ
Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.
آية رقم 30
ﭽﭾﭿﮀ
ﮁ
Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa* take.
* Ranar kora mutane, kamar ana gargaɗa tumãki, zuwa ga tsayuwa a gaba ga Allah, dõmin hisabi.
آية رقم 31
ﮂﮃﮄﮅ
ﮆ
To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!
آية رقم 32
ﮇﮈﮉ
ﮊ
Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!
آية رقم 33
ﮋﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
Sa'an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama.
آية رقم 34
ﮑﮒﮓ
ﮔ
Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.
آية رقم 35
ﮕﮖﮗﮘ
ﮙ
Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.
آية رقم 36
ﮚﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?
آية رقم 37
ﮠﮡﮢﮣﮤﮥ
ﮦ
Bai kasance iɗgo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)
آية رقم 38
ﮧﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;
آية رقم 39
ﮭﮮﮯﮰﮱ
ﯓ
Sa'an nan, Ya sanya daga gare shi, nau'i biyu: namiji damace?
آية رقم 40
Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?*
* Ana son mai karãtu a nan ya ce: a ɓoye بلى وأنا على ذلك من الشاهدين.
تقدم القراءة