سورة عبس

الترجمة الهوساوية

ترجمة معاني سورة عبس باللغة الهوساوية من كتاب الترجمة الهوساوية

الترجمة الهوساوية

الناشر

مجمع الملك فهد

آية رقم 1
Yã game huska* kuma ya jũya bãya.
  * Wani makãho, Abdullahi bin Ummi Maktũm ya je wurin Annabi dõmin ya musulunta, sai ya iske a lõkacin nan Annabi na ƙõƙarin shiryar da wasu manyan mutãne na Ƙuraishãwa, sai wannan makãhon ya yanke maganar Annabi da su, bã da saninsa ba, alhãli Annabi na bũrin su musulunta dõmin darajarsu ga idon mutãnensu. Saboda haka Annabi, (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), ya ɓata Fuska, ya tafi dõmin ɓacin ransa, saboda rashin musuluntarsu. Bãyan haka Annabi nã girmama Abdullahi ƙwarai, idan ya je wurinsa sai ya ce masa "Maraba da wanda Ubangijina Ya zarge ni sabõda shi." Kuma ya shimfiɗa masa mayafinsa, idan ya fita tafiya, yakan sanya shi riƙon garin Madina, ƙissar tana nũna girmamawar Allah ga Annabi da Ya ce: "Ya game Fuska." Bai ce masa: "Domin ka game Fuska" ba, sai ya faɗa a cikin hali mai sauƙi.".
آية رقم 3
To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.
آية رقم 6
Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!
آية رقم 9
Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.
آية رقم 11
A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.
آية رقم 12
Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).
آية رقم 13
(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,
آية رقم 14
Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.
آية رقم 15
A cikin hannãyen mala'iku marubũta.
آية رقم 16
Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.
آية رقم 17
An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!
آية رقم 19
Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).
آية رقم 20
Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.
آية رقم 21
Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.
آية رقم 23
Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).
آية رقم 27
Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.
آية رقم 29
Da zaitũni da itãcen dabĩno.
آية رقم 30
Da lambuna, mãsu yawan itãce.
آية رقم 31
Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.
آية رقم 32
Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.
آية رقم 33
To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.
آية رقم 37
Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.
آية رقم 38
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.
آية رقم 39
Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.
آية رقم 40
Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.
آية رقم 42
Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).
تقدم القراءة