ترجمة معاني سورة عبس باللغة الهوساوية من كتاب الترجمة الهوساوية
آية رقم 1
ﭑﭒ
ﭓ
Yã game huska* kuma ya jũya bãya.
* Wani makãho, Abdullahi bin Ummi Maktũm ya je wurin Annabi dõmin ya musulunta, sai ya iske a lõkacin nan Annabi na ƙõƙarin shiryar da wasu manyan mutãne na Ƙuraishãwa, sai wannan makãhon ya yanke maganar Annabi da su, bã da saninsa ba, alhãli Annabi na bũrin su musulunta dõmin darajarsu ga idon mutãnensu. Saboda haka Annabi, (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), ya ɓata Fuska, ya tafi dõmin ɓacin ransa, saboda rashin musuluntarsu. Bãyan haka Annabi nã girmama Abdullahi ƙwarai, idan ya je wurinsa sai ya ce masa "Maraba da wanda Ubangijina Ya zarge ni sabõda shi." Kuma ya shimfiɗa masa mayafinsa, idan ya fita tafiya, yakan sanya shi riƙon garin Madina, ƙissar tana nũna girmamawar Allah ga Annabi da Ya ce: "Ya game Fuska." Bai ce masa: "Domin ka game Fuska" ba, sai ya faɗa a cikin hali mai sauƙi.".
آية رقم 2
ﭔﭕﭖ
ﭗ
Sabõda makãho yã je masa.
آية رقم 3
ﭘﭙﭚﭛ
ﭜ
To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.
آية رقم 4
ﭝﭞﭟﭠ
ﭡ
Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?
آية رقم 5
ﭢﭣﭤ
ﭥ
Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.
آية رقم 6
ﭦﭧﭨ
ﭩ
Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!
آية رقم 7
ﭪﭫﭬﭭ
ﭮ
To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?
آية رقم 8
ﭯﭰﭱﭲ
ﭳ
Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.
آية رقم 9
ﭴﭵ
ﭶ
Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.
آية رقم 10
ﭷﭸﭹ
ﭺ
Kai kuma kã shagala ga barinsa!
آية رقم 11
ﭻﭼﭽ
ﭾ
A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.
آية رقم 12
ﭿﮀﮁ
ﮂ
Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).
آية رقم 13
ﮃﮄﮅ
ﮆ
(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,
آية رقم 14
ﮇﮈ
ﮉ
Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.
آية رقم 15
ﮊﮋ
ﮌ
A cikin hannãyen mala'iku marubũta.
آية رقم 16
ﮍﮎ
ﮏ
Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.
آية رقم 17
ﮐﮑﮒﮓ
ﮔ
An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!
آية رقم 18
ﮕﮖﮗﮘ
ﮙ
Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?
آية رقم 19
ﮚﮛﮜﮝ
ﮞ
Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).
آية رقم 20
ﮟﮠﮡ
ﮢ
Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.
آية رقم 21
ﮣﮤﮥ
ﮦ
Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.
آية رقم 22
ﮧﮨﮩﮪ
ﮫ
Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.
آية رقم 23
ﮬﮭﮮﮯﮰ
ﮱ
Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).
آية رقم 24
ﯓﯔﯕﯖ
ﯗ
To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.
آية رقم 25
ﯘﯙﯚﯛ
ﯜ
Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.
آية رقم 26
ﯝﯞﯟﯠ
ﯡ
Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.
آية رقم 27
ﯢﯣﯤ
ﯥ
Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.
آية رقم 28
ﯦﯧ
ﯨ
Da inabi da ciyãwa.
آية رقم 29
ﯩﯪ
ﯫ
Da zaitũni da itãcen dabĩno.
آية رقم 30
ﯬﯭ
ﯮ
Da lambuna, mãsu yawan itãce.
آية رقم 31
ﯯﯰ
ﯱ
Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.
آية رقم 32
ﯲﯳﯴ
ﯵ
Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.
آية رقم 33
ﯶﯷﯸ
ﯹ
To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.
آية رقم 34
ﯺﯻﯼﯽﯾ
ﯿ
Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.
آية رقم 35
ﰀﰁ
ﰂ
Da uwarsa da ubansa.
آية رقم 36
ﰃﰄ
ﰅ
Da mãtarsa da ɗiyansa.
آية رقم 37
ﰆﰇﰈﰉﰊﰋ
ﰌ
Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.
آية رقم 38
ﰍﰎﰏ
ﰐ
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.
آية رقم 39
ﰑﰒ
ﰓ
Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.
آية رقم 40
ﰔﰕﰖﰗ
ﰘ
Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.
آية رقم 41
ﭑﭒ
ﭓ
Baƙi zai rufe su.
آية رقم 42
ﭔﭕﭖﭗ
ﭘ
Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).
تقدم القراءة