سورة الليل

الترجمة الهوساوية

ترجمة معاني سورة الليل باللغة الهوساوية من كتاب الترجمة الهوساوية

الترجمة الهوساوية

الناشر

مجمع الملك فهد

آية رقم 1
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.
آية رقم 2
Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.
آية رقم 6
Kuma ya gaskata kalma* mai kyãwo.
 * Kalma mai kyãwo ita ce Kalmar shahãda da abin da ta ƙunsa na addinin Musulunci, wanda yake yinsa kamar yadda Allah Ya ce, ta hanyan ManzonSa, shi ne taƙawa.
آية رقم 7
To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.
آية رقم 8
Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.
آية رقم 9
Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.
آية رقم 10
To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.
آية رقم 11
Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).
آية رقم 12
Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.
آية رقم 14
Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.
آية رقم 16
Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya.
آية رقم 17
Kuma mafi taƙawa* zai nisance ta.
 * Mafi taƙawa da Mafi shaƙãwa suna ma'anar mai taƙawa da shaƙiyyi.
آية رقم 18
Wanda yake bãyar da dũkiyarsa, alhãli yana tsarkaka.
آية رقم 21
To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi).
تقدم القراءة