ترجمة معاني سورة الأعلى باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﮟﮠﮡﮢ
ﮣ
Al'A'alah
Ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mafi ɗaukaka.
آية رقم 2
ﮤﮥﮦ
ﮧ
Wanda Yã yi halitta sa'an nan Ya daidaita abin halittar.
آية رقم 3
ﮨﮩﮪ
ﮫ
Kuma Wanda Ya ƙaddara (abin da Ya so) sannan Ya shiryar, (da mutum ga hanyar alhẽri da ta sharri).
آية رقم 4
ﮬﮭﮮ
ﮯ
Kuma Wanda Ya fitar da makiyãyã.
آية رقم 5
ﮰﮱﯓ
ﯔ
Sa'an nan Ya mayar da ita ƙeƙasassa, baƙa.
آية رقم 6
ﯕﯖﯗ
ﯘ
Za mu karantar da kai (Alƙur'ãni) sabõda haka bã zã ka mantã (shi) ba.
آية رقم 7
Fãce abin da Allah Ya so, lalle ne Shi (Allah) Ya san bayyane da abin da yake bõye.
آية رقم 8
ﯤﯥ
ﯦ
Kuma za Mu sauƙaƙe maka (al'amari) zuwa ga (Shari'a) mai sauƙi.
آية رقم 9
ﯧﯨﯩﯪ
ﯫ
Sabõda baka, ka tunãtar, idan tunatarwa zã ta yi amfãni.
آية رقم 10
ﯬﯭﯮ
ﯯ
Wanda yake tsõron (Allah) Zai tuna.
آية رقم 11
ﭑﭒ
ﭓ
Kuma shaƙiyyi, zai nisanceta,
آية رقم 12
ﭔﭕﭖﭗ
ﭘ
Wanda zai shiga wutar da tã fi girma.
آية رقم 13
ﭙﭚﭛﭜﭝﭞ
ﭟ
Sa'an nan bã zai mutu ba a cikinta, kuma bã zai rãyu ba.
آية رقم 14
ﭠﭡﭢﭣ
ﭤ
Lalle ne wanda ya tsarkaka (da ĩmãni) yã sãmu babban rabo.
آية رقم 15
ﭥﭦﭧﭨ
ﭩ
Kuma ya ambaci sũnan Ubangijinsa, sa'an nan yã yi salla.
آية رقم 16
ﭪﭫﭬﭭ
ﭮ
Ba haka ba! Kunã zãɓin rãyuwa ta kusa dũniya.
آية رقم 17
ﭯﭰﭱ
ﭲ
Alhãli Lãhira ita ce mafi alheri kuma mafi wanzuwa.
آية رقم 18
ﭳﭴﭵﭶﭷ
ﭸ
Lalle ne, wannan yanã a cikin littafan farko.
آية رقم 19
ﭹﭺﭻ
ﭼ
Littaffan Ibrãhĩm da Mũsã.
تقدم القراءة