ترجمة معاني سورة الواقعة باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

آية رقم 2

Bãbu wani (rai) mai ƙaryatãwa ga aukuwarta.
آية رقم 3

(Ita) mai ƙasƙantãwa ce, mai ɗaukakãwa.
آية رقم 6

Sai suka kasance ƙũra da ake wãtsarwa.
آية رقم 10

Da waɗanda suka tsẽre. Sũ wɗanda suka tsẽren nan,
آية رقم 11

Waɗancan, sũ ne waɗanda aka kusantar.
آية رقم 15

(Sunã) a kan wasu gadãje sãƙaƙƙuu.
آية رقم 16

Sunã gincire a kansu, sunã mãsu kallon jũna.
آية رقم 18

Da wasu kõfuna da shantula da hinjãlai daga (giya) mai ɓuɓɓuga.
آية رقم 19

Bã a sanya musu cĩwon jirĩ sabõda ita, kuma bã su buguwa.
آية رقم 20

Da wasu 'ya'yan itãcen marmari daga irin waɗanda suke zãɓe.
آية رقم 21

Da nãman tsuntsãye daga wanda suke ganin sha'awa.
آية رقم 22

Da wasu mãtã mãsu fararen idanu da girmansu.
آية رقم 23

Kamar misãlan lu'ulu'u wanda aka ɓõye.
آية رقم 24

A kan sakamakon, dõmin abin da suka kasance sunã aikatãwa.
آية رقم 26

Sai dai wata magana (mai dãɗi): Salãmun, Salãmun.
آية رقم 28

(Sunã) a cikin itãcen magarya maras ƙaya.
آية رقم 29

Da wata ayaba mai yawan 'ya'ya.
آية رقم 30

Da wata inuwa mĩƙaƙƙiya.
آية رقم 32

Da wasu 'ya'yan itacen marmari mãsu yawa.
آية رقم 34

Da wasu shimfiɗu maɗaukaka.
آية رقم 35

Lalle Mũ, Mun ƙãga halittarsu ƙãgãwa.
آية رقم 36

Sa'an nan Muka sanya su budurwai.
آية رقم 37

Mãsu son mazansu, a cikin tsãrã ɗaya.
آية رقم 40

Da wata ƙungiya daga mutãnen ƙarshe.
آية رقم 42

Sunã a cikin wata iskar zãfi da wani ruwan zãfi.
آية رقم 45

Lalle sũ, sun kasance a gabãnin wannan waɗanda aka jiyar dãɗi.
آية رقم 46

Kuma sun kasance sunã dõgẽwa a kan mummũnan zunubi mai girma.

Kuma sun kasance sunã cẽwa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓãya da ƙasũsuwa shin lalle mũ waɗanda zã a kõma rãyarwa ne haƙĩƙatan?"
آية رقم 48

"Shin, kuma da ubanninmu na farko?"
آية رقم 52

"Lalle mãsu cĩ ne daga wata itãciya ta zaƙƙum (ɗanyen wutã)."
آية رقم 53

"Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."
آية رقم 54

"Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."
آية رقم 55

"Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."
آية رقم 57

Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba?
آية رقم 58

Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?
آية رقم 59

Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa?
آية رقم 62

Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?
آية رقم 63

Shin, kuma kun ga abin da kũke nõmãwa?
آية رقم 65

Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.
آية رقم 66

(Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"
آية رقم 67

"Ã'a, mun dai zama waɗanda aka hanã wa!"
آية رقم 70

Dã Mun so, dã Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me bã ku gõdẽwa?
آية رقم 71

Shin, kuma kun ga wutã wannan da kuke ƙyastãwa?
آية رقم 72

Shin, kũ ne kuke ƙagã halittar itãciyarta, kõ kuwa Mũ ne Mãsu ƙãgãwa?
آية رقم 73

Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.
آية رقم 76

Kuma lalle ne' haƙĩƙa, rantsuwa ce mai girma, dã kun sani.
آية رقم 77

Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja.
آية رقم 81

Shin, to, wannan lãbãrin ne kuke mãsu wulãkantãwa?
آية رقم 82

Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)?
آية رقم 83

To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa).
آية رقم 84

Alhãli kuwa kũ, a lõklcin nan, kunã kallo.
آية رقم 86

To, don me in dai kun kasance bã waɗanda zã a yi wa sakamako ba?
آية رقم 87

Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya.
آية رقم 89

Sai hũtawa da kyakkyawan abinci da Aljannar ni'ima.
آية رقم 91

Sai (a ce masa) aminci ya tabbata a gare ka daga mazõwa dãma.
آية رقم 96

Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangijinka, Mai karimci.
تقدم القراءة