ترجمة معاني سورة الدّخان باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﭑ
ﭒ
Ad-Dukhan
Ḥ. M̃.
آية رقم 2
ﭓﭔ
ﭕ
Inã rantsuwa da Littãfi Mabayyani.
آية رقم 3
Lalle ne, Mũ, Muka saukar da shi a cikin wani dare mai albarka. Lalle Mũ' Mun kasance Mãsu yin gargaɗi.
آية رقم 4
ﭠﭡﭢﭣﭤ
ﭥ
A cikinsa (shi daren) ake rarrabe kõwane umurui bayyananne.
آية رقم 5
Umurni na daga wurinMu. Lalle Mũ ne Muka kasanceMãsu aikãwã.
آية رقم 6
Sabõda rahama daga Ubangijinka. Lalle Shĩ, Shi ne Mai ji, Mãsani.
آية رقم 7
(Shĩ ne) Ubangijin sammai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu yaƙĩni (za ku gãne haka).
آية رقم 8
Babu abin bautãwa fãce Shi. Yana rãyarwa Kuma Yana kashẽwa. (Shi ne) Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko.
آية رقم 9
ﮍﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
A'a sũ, sunã wãsã a cikin shakka.
آية رقم 10
ﮓﮔﮕﮖﮗﮘ
ﮙ
Sabõda haka, ka dakata rãnar da sama zã tã zo da hayãƙi bayyananne.
آية رقم 11
ﮚﮛﮜﮝﮞﮟ
ﮠ
Yanã rufe mutãne. Wannan wata azãba ce mai raɗaɗi.
آية رقم 12
ﮡﮢﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
Ya Ubangijinmu! Ka kuranye mana azãba. Lalle Mũ, mãsu ĩmãni ne.
آية رقم 13
Inã tunãwa take a gare su, alhãli kuwa, haƙĩƙa, Manzo mai bayyanãwa Ya je musu (da gargaɗin saukar azãbar, ba su karɓa ba)?
آية رقم 14
ﮰﮱﯓﯔﯕﯖ
ﯗ
Sa'an nan suka jũya baya daga gare shi, Kuma suka ce: "Wanda ake gayãwa ne, mahaukaci."
آية رقم 15
Lalle Mũ, Mãsu kuranyẽwar azãba ne, a ɗan lõkaci kaɗan, lalle kũ, mãsu kõmãwa ne (ga laifin).
آية رقم 16
ﯠﯡﯢﯣﯤﯥ
ﯦ
Rãnar da Muke damƙa, damƙa mafi girma, lalle ne Mũ mãsu azãbar rãmuwa ne.
آية رقم 17
Kuma lalle ne haƙĩƙa a gabaninsu, Mun fitini mutãnen Fir'auna, kuma wani Manzo karĩmi ya jẽ musu.
آية رقم 18
(Mazon ya ce): "Ku kãwo mini (ĩmãninku) ya bayin Allah! Lalle ni, Manzo ne amintacce zuwa gare ku."
آية رقم 19
"Kuma kada ku nẽmi ɗaukaka a kan Allah. Lalle nĩ mai zo muku ne da dalĩli bayyananne."
آية رقم 20
ﭜﭝﭞﭟﭠﭡ
ﭢ
"Kuma lalle nĩ na nẽmi tsari da Ubangijĩna, kuma Ubangijinku, dõmin kada ku jẽfe ni."
آية رقم 21
ﭣﭤﭥﭦﭧ
ﭨ
"Kuma idan ba ku yi ĩmãni sabõda nĩ ba, to, ku nĩsance ni."
آية رقم 22
ﭩﭪﭫﭬﭭﭮ
ﭯ
Sai ya kirayi Ubangjinsa cẽwa waɗannan mutãnene mãsu laifi.
آية رقم 23
ﭰﭱﭲﭳﭴ
ﭵ
(Allah Ya ce): "To, ka yi tafiyar dare da bayiNa, da dare. Lalle kũ, waɗanda ake bĩ ne (dõmin a kãma ku.)"
آية رقم 24
"Kuma ka bar tẽku rarrabe. Lalle sũ, runduna ce abar nutsarwa."
آية رقم 25
ﭾﭿﮀﮁﮂ
ﮃ
Da yawa suka bar gõnaki da marẽmari.
آية رقم 26
ﮄﮅﮆ
ﮇ
Da shuke-shuke da matsayi mai kyau.
آية رقم 27
ﮈﮉﮊﮋ
ﮌ
Da wata ni'ima da suka kasance a cikinta sunã mãsu hutu.
آية رقم 28
ﮍﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da ita ga waɗansu mutãne na dabam.
آية رقم 29
Sa'an nan samã da ƙasã ba su yi kũka a kansu ba, Kuma ba su kasance waɗanda ake yi wa jinkiri ba.
آية رقم 30
Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun tsĩrar da Banĩ Isrã'ĩla daga, azãba mai wulãkantãwa.
آية رقم 31
Daga Fir'auna. Lalle shi, ya kasance maɗaukaki daga cikin mãsu ɓarna.
آية رقم 32
ﮭﮮﮯﮰﮱﯓ
ﯔ
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe su sabõda wani ilmi (na Taurata) a kan mutãne.
آية رقم 33
Kuma Muka bã su, daga ãyõyin mu'ujizõji, abin da yake a cikinsa, akwai ni'ima bayyananna
آية رقم 34
ﯝﯞﯟ
ﯠ
Lalle waɗannan mutãne, haƙĩka, sunã cẽwa,
آية رقم 35
"Babu wani abu sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake tãyarwa ba."
آية رقم 36
ﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
"Sai ku zo da ubanninmu, idan kun kasance mãsu gaskiya."
آية رقم 37
shin, sũ ne mafĩfĩta kõ kuwa mutãnen Tubba'u, kuma da waɗanda ke a gabãninsu? Mun halaka su, lalle sũ, sun kasance mãsu laifi.
آية رقم 38
Kuma ba Mu halitta slmmai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu ba, alhãli kuwa Munã mãsu wãsã.
آية رقم 39
Ba Mu halitta su ba fãce da manufa ta gaskiya, kuma amma mafi yawansu, ba su sani ba.
آية رقم 40
ﭑﭒﭓﭔﭕ
ﭖ
Lalle rãnar rarrabẽwa, ita ce lõkacin wa'adinsu gabã ɗaya.
آية رقم 41
Rãnar da wani zumu bã ya amfãnin wani zumu da kõme kuma ba su zama anã taimakon su ba.
آية رقم 42
fãce wanda Allah Ya yi wa rahama. Lalle Shi (Allah), shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
آية رقم 43
ﭫﭬﭭ
ﭮ
Lalle itãciyar zaƙƙũm (ɗanyen wutã),
آية رقم 44
ﭯﭰ
ﭱ
Ita ce abincin mai laifi.
آية رقم 45
ﭲﭳﭴﭵ
ﭶ
Kamar narkakken kwalta yanã tafasa a cikin cikunna.
آية رقم 46
ﭷﭸ
ﭹ
Kamar tafasar ruwan zãfi.
آية رقم 47
ﭺﭻﭼﭽﭾ
ﭿ
(A cẽ wa malã'ikun wutã), "Ku kãmã shi, sa'an nan ku fizge shi zuwa ga tsakiyar Jahĩm."
آية رقم 48
"Sa'an nan ku zuba, a kansa, daga azãbar ruwan zãfi."
آية رقم 49
ﮈﮉﮊﮋﮌ
ﮍ
(A ce masã), "Ka ɗanɗana! Lalle kai, kai ne mabuwãyi mai girma!"
آية رقم 50
ﮎﮏﮐﮑﮒﮓ
ﮔ
"Lalle wannan, shi ne abin da kuka kasance kunã shakka game da shi."
آية رقم 51
ﮕﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
Lalle mãsu taƙawa sunã cikin matsayi amintacce.
آية رقم 52
ﮛﮜﮝ
ﮞ
A cikin gidãjen Aljanna da marẽmari.
آية رقم 53
ﮟﮠﮡﮢﮣ
ﮤ
Sunã tufanta daga tufãfin alharĩni raƙĩƙi, da mai kauri, sunã mãsu zaman fuskantar jũna.
آية رقم 54
ﮥﮦﮧﮨ
ﮩ
Kamar haka, kuma Mun aurar da su da mãtã mãsu kyaun idãnu, mãsu girmansu.
آية رقم 55
ﮪﮫﮬﮭﮮ
ﮯ
Sunã kira, a cikinsu (gidẽjen) ga dukan 'ya'yan itãcen marmari, sunã amintattu (daga dukan abin tsõro).
آية رقم 56
Bã su ɗanɗanar mutuwa, a cikinsu, fãce mutuwar farko, kuma (Allah), Ya tsare musu azãbar Jahĩm.
آية رقم 57
Sabõda falala daga Ubangijinka. Wancan shi ne babban rabo, mai girma.
آية رقم 58
ﯦﯧﯨﯩﯪ
ﯫ
Dõmin haka kawai Muka sauƙaƙar da shi (Alƙur'ãni) da harshenka, tsammãninsu, su riƙa tunãwa.
آية رقم 59
ﯬﯭﯮ
ﯯ
Sai ka yi jira. Lalle sũ, mãsu jira ne.
تقدم القراءة