ترجمة معاني سورة الدّخان باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

آية رقم 1

Ad-Dukhan


Ḥ. M̃.
آية رقم 2

Inã rantsuwa da Littãfi Mabayyani.

(Shĩ ne) Ubangijin sammai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu yaƙĩni (za ku gãne haka).
آية رقم 13

Inã tunãwa take a gare su, alhãli kuwa, haƙĩƙa, Manzo mai bayyanãwa Ya je musu (da gargaɗin saukar azãbar, ba su karɓa ba)?
آية رقم 14

Sa'an nan suka jũya baya daga gare shi, Kuma suka ce: "Wanda ake gayãwa ne, mahaukaci."
آية رقم 15

Lalle Mũ, Mãsu kuranyẽwar azãba ne, a ɗan lõkaci kaɗan, lalle kũ, mãsu kõmãwa ne (ga laifin).
آية رقم 16

Rãnar da Muke damƙa, damƙa mafi girma, lalle ne Mũ mãsu azãbar rãmuwa ne.
آية رقم 20

"Kuma lalle nĩ na nẽmi tsari da Ubangijĩna, kuma Ubangijinku, dõmin kada ku jẽfe ni."
آية رقم 21

"Kuma idan ba ku yi ĩmãni sabõda nĩ ba, to, ku nĩsance ni."
آية رقم 23

(Allah Ya ce): "To, ka yi tafiyar dare da bayiNa, da dare. Lalle kũ, waɗanda ake bĩ ne (dõmin a kãma ku.)"
آية رقم 27

Da wata ni'ima da suka kasance a cikinta sunã mãsu hutu.
آية رقم 28

Kamar haka! Kuma Muka gãdar da ita ga waɗansu mutãne na dabam.
آية رقم 29

Sa'an nan samã da ƙasã ba su yi kũka a kansu ba, Kuma ba su kasance waɗanda ake yi wa jinkiri ba.
آية رقم 30

Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun tsĩrar da Banĩ Isrã'ĩla daga, azãba mai wulãkantãwa.
آية رقم 32

Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe su sabõda wani ilmi (na Taurata) a kan mutãne.
آية رقم 33

Kuma Muka bã su, daga ãyõyin mu'ujizõji, abin da yake a cikinsa, akwai ni'ima bayyananna
آية رقم 34

Lalle waɗannan mutãne, haƙĩka, sunã cẽwa,
آية رقم 38

Kuma ba Mu halitta slmmai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu ba, alhãli kuwa Munã mãsu wãsã.
آية رقم 40

Lalle rãnar rarrabẽwa, ita ce lõkacin wa'adinsu gabã ɗaya.
آية رقم 43

Lalle itãciyar zaƙƙũm (ɗanyen wutã),
آية رقم 45

Kamar narkakken kwalta yanã tafasa a cikin cikunna.
آية رقم 46

Kamar tafasar ruwan zãfi.
آية رقم 47

(A cẽ wa malã'ikun wutã), "Ku kãmã shi, sa'an nan ku fizge shi zuwa ga tsakiyar Jahĩm."
آية رقم 49

(A ce masã), "Ka ɗanɗana! Lalle kai, kai ne mabuwãyi mai girma!"
آية رقم 52

A cikin gidãjen Aljanna da marẽmari.
آية رقم 53

Sunã tufanta daga tufãfin alharĩni raƙĩƙi, da mai kauri, sunã mãsu zaman fuskantar jũna.
آية رقم 54

Kamar haka, kuma Mun aurar da su da mãtã mãsu kyaun idãnu, mãsu girmansu.
آية رقم 55

Sunã kira, a cikinsu (gidẽjen) ga dukan 'ya'yan itãcen marmari, sunã amintattu (daga dukan abin tsõro).
آية رقم 58

Dõmin haka kawai Muka sauƙaƙar da shi (Alƙur'ãni) da harshenka, tsammãninsu, su riƙa tunãwa.
آية رقم 59

Sai ka yi jira. Lalle sũ, mãsu jira ne.
تقدم القراءة