ترجمة معاني سورة الذاريات باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

آية رقم 1

Az-Zariyat


Inã rantsuwa da iskõki mãsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.
آية رقم 2

Sa'an nan da girãgizai mãsu ɗaukar nauyi (na ruwa).
آية رقم 3

Sa'an nan da jirãge mãsu gudãna (a kan ruwa) da sauƙi.
آية رقم 4

Sa'an nan da Malã'iku mãsu rabon al'amari (bisa umurnin Allah).
آية رقم 5

Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.
آية رقم 6

Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne
آية رقم 7

Inã rantsuwa da samã ma'abũciyar hanyõyi (na tafiyar taurãri da sautin rediyo).
آية رقم 8

Lalle kũ, haƙĩƙa, kunã cikin magana mai sãɓa wa juna (game da Alƙur'ani).
آية رقم 10

An la'ani mãsu ƙiri-faɗi.
آية رقم 12

Sunã tambaya: "Yaushe ne rãnar sakamako zã ta auku?"
آية رقم 14

(A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kunã nẽman zuwansa da gaggãwa."
آية رقم 15

Lalle mãsu taƙawa, sunã a cikin lambunan itãce da marẽmari.
آية رقم 18

Kuma a lõkutan asuba sunã ta yin istigfãri.
آية رقم 19

Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hana wa rõƙo.
آية رقم 20

Kuma a cikin ƙasã akwai ãyõyi ga mãsu yaƙĩni.
آية رقم 21

Kuma a cikin rãyukanku (akwai ãyõyi). To, bã zã ku dũbã ba?
آية رقم 22

Kuma a cikin sama arzikinku (yake fitõwa) da abin da ake yi muku alkawari.

To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasã, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kunã karantãwa na magana,
آية رقم 27

Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bã zã ku ci ba?"

Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallõwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsõhuwa bakarãriya (zã ta haihu)!"
آية رقم 34

"Waɗanda aka yi wa alãma daga wajen Ubangijinka, dõmin mãsu ɓarna."
آية رقم 39

Sai ya jũya bãya tãre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kõ kuwa mahaukaci!"
آية رقم 40

Sabõda haka, Muka kama shi tãre da rundunarsa, sa'an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
آية رقم 44

Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabõda haka tsãwa ta kãma su, alhãli kuwa sunã kallo.
آية رقم 47

Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhãli kuwa lalle Mũ ne Mãsu yalwatãwa.
آية رقم 48

Kuma ƙasã Mun shimfiɗa ta, To, madalla da mãsu shimfiɗãwa, Mũ,

To, lalle waɗanda suka yi zãlunci sunã da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abõkansu, sabõda haka kada su yi Mini gaggãwa.
آية رقم 60

Sabõda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta, daga rãnar su wadda aka yi musu alkawari.
تقدم القراءة