ترجمة معاني سورة الذاريات باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﯤﯥ
ﯦ
Az-Zariyat
Inã rantsuwa da iskõki mãsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.
آية رقم 2
ﯧﯨ
ﯩ
Sa'an nan da girãgizai mãsu ɗaukar nauyi (na ruwa).
آية رقم 3
ﯪﯫ
ﯬ
Sa'an nan da jirãge mãsu gudãna (a kan ruwa) da sauƙi.
آية رقم 4
ﯭﯮ
ﯯ
Sa'an nan da Malã'iku mãsu rabon al'amari (bisa umurnin Allah).
آية رقم 5
ﯰﯱﯲ
ﯳ
Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.
آية رقم 6
ﯴﯵﯶ
ﯷ
Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne
آية رقم 7
ﭑﭒﭓ
ﭔ
Inã rantsuwa da samã ma'abũciyar hanyõyi (na tafiyar taurãri da sautin rediyo).
آية رقم 8
ﭕﭖﭗﭘ
ﭙ
Lalle kũ, haƙĩƙa, kunã cikin magana mai sãɓa wa juna (game da Alƙur'ani).
آية رقم 9
ﭚﭛﭜﭝ
ﭞ
Anã karkatar da wanda aka jũyar (daga gaskiya).
آية رقم 10
ﭟﭠ
ﭡ
An la'ani mãsu ƙiri-faɗi.
آية رقم 11
ﭢﭣﭤﭥﭦ
ﭧ
Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jãhilci.
آية رقم 12
ﭨﭩﭪﭫ
ﭬ
Sunã tambaya: "Yaushe ne rãnar sakamako zã ta auku?"
آية رقم 13
ﭭﭮﭯﭰﭱ
ﭲ
Ranar da suke a kan wuta anã fitinar su.
آية رقم 14
(A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kunã nẽman zuwansa da gaggãwa."
آية رقم 15
ﭻﭼﭽﭾﭿ
ﮀ
Lalle mãsu taƙawa, sunã a cikin lambunan itãce da marẽmari.
آية رقم 16
Sunã mãsu dĩbar abin da Ubangijinsu Ya bã su. Lalle sũ, sun kasance mãsu kyautatãwa a gabãnin haka (a dũniya).
آية رقم 17
ﮌﮍﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
Sun kasance a lõkaci kaɗan na dare suke yin barci.
آية رقم 18
ﮓﮔﮕ
ﮖ
Kuma a lõkutan asuba sunã ta yin istigfãri.
آية رقم 19
ﮗﮘﮙﮚﮛ
ﮜ
Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hana wa rõƙo.
آية رقم 20
ﮝﮞﮟﮠ
ﮡ
Kuma a cikin ƙasã akwai ãyõyi ga mãsu yaƙĩni.
آية رقم 21
ﮢﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
Kuma a cikin rãyukanku (akwai ãyõyi). To, bã zã ku dũbã ba?
آية رقم 22
ﮨﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
Kuma a cikin sama arzikinku (yake fitõwa) da abin da ake yi muku alkawari.
آية رقم 23
To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasã, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kunã karantãwa na magana,
آية رقم 24
ﯙﯚﯛﯜﯝﯞ
ﯟ
Shin, lãbãrin Bãƙin Ibrãhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka?
آية رقم 25
A lõkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutãne bãƙi!"
آية رقم 26
ﯫﯬﯭﯮﯯﯰ
ﯱ
Sai ya jũya zuwa ga iyãlinsa, sa'an nan ya zo da maraƙi tutturna,
آية رقم 27
ﯲﯳﯴﯵﯶ
ﯷ
Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bã zã ku ci ba?"
آية رقم 28
Sai ya ji tsõro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsõro." Kuma suka yi masa bushãra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi.
آية رقم 29
Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallõwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsõhuwa bakarãriya (zã ta haihu)!"
آية رقم 30
Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai hikima, Mai ilmi."
آية رقم 31
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
(Ibrãĩm) ya ce: "To mẽne ne babban al'almarinku, yã kũ Manzanni!"
آية رقم 32
ﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
ﭞ
Suka ce: "Lalle mũ, an aike mu zuwa ga waɗansu mutãne, mãsu laifi.
آية رقم 33
ﭟﭠﭡﭢﭣ
ﭤ
"Dõmin mu saka musu waɗansu duwãtsu na wani yumɓu (bom).
آية رقم 34
ﭥﭦﭧﭨ
ﭩ
"Waɗanda aka yi wa alãma daga wajen Ubangijinka, dõmin mãsu ɓarna."
آية رقم 35
ﭪﭫﭬﭭﭮﭯ
ﭰ
Sa'an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga mũminai.
آية رقم 36
Sai dai ba mu sãmu ba, a cikinta, fãce gida guda na Musulmi.
آية رقم 37
Kuma Muka bar wata ãyã, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsõron azãba, mai raɗaɗi.
آية رقم 38
Kuma ga Mũsã, a lõkacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da wani dalĩli bayyananne.
آية رقم 39
ﮊﮋﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
Sai ya jũya bãya tãre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kõ kuwa mahaukaci!"
آية رقم 40
Sabõda haka, Muka kama shi tãre da rundunarsa, sa'an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
آية رقم 41
Kuma ga Ãdãwa, a lõkacin da Muka aika iska ƙẽƙasasshiya a kansu.
آية رقم 42
Bã ta barin kõme da ta jẽ a kansa, fãce ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasũsuwa.
آية رقم 43
Kuma ga Samũdãwa, a lõkacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan dãɗi har wani ɗan lõkaci,"
آية رقم 44
Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabõda haka tsãwa ta kãma su, alhãli kuwa sunã kallo.
آية رقم 45
Ba su kõ sãmu dãmar tsayãwa ba, kuma ba su kasance mãsu nẽman ãgaji ba.
آية رقم 46
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutãne ne fãsiƙai.
آية رقم 47
ﯰﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhãli kuwa lalle Mũ ne Mãsu yalwatãwa.
آية رقم 48
ﯶﯷﯸﯹ
ﯺ
Kuma ƙasã Mun shimfiɗa ta, To, madalla da mãsu shimfiɗãwa, Mũ,
آية رقم 49
Kuma daga kõme Mun halitta nau'i biyu, watakila zã ku yi tunãni.
آية رقم 50
Sabõda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle nĩ mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
آية رقم 51
Kuma kada ku sanya, tãre da Allah wani abin bautãwa na dabam, lalle nĩ, mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
آية رقم 52
Kamar haka dai wani Manzo bai jẽ wa waɗanda ke gabãninsu ba fãce sun ce: "Mai sihiri ne kõ mahaukaci."
آية رقم 53
shin, sunã yi wa jũna wasiyya da shi ne? Ã'a, sũ dai mutãne ne mãsu girman kai.
آية رقم 54
ﭧﭨﭩﭪﭫ
ﭬ
Sai ka jũya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne.
آية رقم 55
ﭭﭮﭯﭰﭱ
ﭲ
Kuma ka tunãtar, dõmin tunãtarwa tanã amfãnin mũminai.
آية رقم 56
ﭳﭴﭵﭶﭷﭸ
ﭹ
Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini.
آية رقم 57
Bã Ni nufln (sãmun) wani arziki daga gare su, Bã Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni.
آية رقم 58
Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.
آية رقم 59
To, lalle waɗanda suka yi zãlunci sunã da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abõkansu, sabõda haka kada su yi Mini gaggãwa.
آية رقم 60
Sabõda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta, daga rãnar su wadda aka yi musu alkawari.
تقدم القراءة