ترجمة معاني سورة العاديات باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﮱﯓ
ﯔ
Al-Adiyat
Ina rantsuwa da dawãki mãsu gudu suna fitar da kũkan ciki.
آية رقم 2
ﯕﯖ
ﯗ
Mãsu ƙyasta wuta (da kõfatansu a kan duwatsu) ƙyastawa.
آية رقم 3
ﯘﯙ
ﯚ
Sa'an nan mãsu yin hari a lokacin asuba.
آية رقم 4
ﯛﯜﯝ
ﯞ
Sai su motsar da ƙũra game da shi.
آية رقم 5
ﯟﯠﯡ
ﯢ
Sai su shiga, game da ita (ƙũrar), a tsakãnin jama'ar maƙiya.
آية رقم 6
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Lalle ne mutum mai tsananin butulci ne ga Ubangijinsa.
آية رقم 7
ﭖﭗﭘﭙ
ﭚ
Lalle ne shi mai shaida ne a kan laifinsa dl haka.
آية رقم 8
ﭛﭜﭝﭞ
ﭟ
Kuma 1alle ne ga dũkiya shi mai tsananin so ne.
آية رقم 9
Shin, bã ya da sanin lõkacin da aka tõne abin da yake cikin kaburbura.
آية رقم 10
ﭩﭪﭫﭬ
ﭭ
Aka bayyana abin da ke cikin zukata.
آية رقم 11
ﭮﭯﭰﭱﭲ
ﭳ
Lalle ne Ubangijinsu, game da su a ranar nan Mai ƙididdigewa ne?
تقدم القراءة