ترجمة سورة الزلزلة

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ترجمة معاني سورة الزلزلة باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation .

Al-zalzalah


Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.

Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.

Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"

A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.

cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.

A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.

To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.

Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.
Icon