ترجمة سورة الزلزلة

الترجمة الهوساوية
ترجمة معاني سورة الزلزلة باللغة الهوساوية من كتاب الترجمة الهوساوية .
من تأليف: أبو بكر محمود جومي .

Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.
Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.
Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"
A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.
cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.
A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.
To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.
Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.
Icon