ترجمة معاني سورة الطور باللغة الهوساوية من كتاب الترجمة الهوساوية
ﰡ
آية رقم 1
ﮞ
ﮟ
Inã rantsuwa da ¦ũr (Dũtsen Mũsã).
آية رقم 2
ﮠﮡ
ﮢ
Da wani littãfi rubũtacce.
آية رقم 3
ﮣﮤﮥ
ﮦ
A cikin wata takardar fãta shimfiɗaɗɗa.
آية رقم 4
ﮧﮨ
ﮩ
Da Gidan da aka rãyar da shi (da ibãda).
آية رقم 5
ﮪﮫ
ﮬ
Da rufin nan da aka ɗaukaka.
آية رقم 6
ﮭﮮ
ﮯ
Da tẽkun nan da aka cika (da ruwa).
آية رقم 7
ﮰﮱﯓﯔ
ﯕ
Lalle, azãbar Ubangijinka, haƙĩƙa, mai aukuwa ce.
آية رقم 8
ﯖﯗﯘﯙ
ﯚ
Bã ta da mai tunkuɗẽwa.
آية رقم 9
ﯛﯜﯝﯞ
ﯟ
Rãnar da samã ke yin mõtsi tanã kai kãwo.
آية رقم 10
ﯠﯡﯢ
ﯣ
Kuma duwãtsu nã tafiya sunã shũɗẽwa.
آية رقم 11
ﯤﯥﯦ
ﯧ
To, bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.
آية رقم 12
ﯨﯩﯪﯫﯬ
ﯭ
Waɗanda suke a cikin kududdufi sunã wãsã.
آية رقم 13
ﯮﯯﯰﯱﯲﯳ
ﯴ
Rãnar da zã a tunkuɗa su zuwa wutar Jahannama, tunkuɗãwa.
آية رقم 14
ﯵﯶﯷﯸﯹﯺ
ﯻ
(A ce musu): "Wannan ita ce wutar da kuka kasance kunã ƙaryatãwa game da ita."
آية رقم 15
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
"To, shin wannan sihiri ne kõ kuwa kũ ne bã ku gani?"
آية رقم 16
"Ku shigẽ ta. To, ku yi haƙuri ko kuma kada ku yi haƙuri, dai dai ne a kanku, kawai anã yi muku sakamakon abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
آية رقم 17
ﭦﭧﭨﭩﭪ
ﭫ
Lalle, mãsu taƙawa, sunã a cikin gidãjen Aljanna da wata ni'ima.
آية رقم 18
Sunã mãsu jin dãɗi da abin da Ubangijinsu Ya ba su, kuma Ubangijinsu Ya tsãre musu azãbar Jahĩm.
آية رقم 19
ﭵﭶﭷﭸﭹﭺ
ﭻ
(A ce musu): "Ku ci, ku sha, da ni'ima, dõmin abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
آية رقم 20
Sunã kishingiɗe a kan karagu waɗanda ke cikin sahu, kuma Muka aurar da su waɗansu mãtã mãsu farin idãnu, mãsu girmansu.
آية رقم 21
Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma zũriyarsu *suka bĩ su ga ĩmãnin, Mun riskar da zũriyarsu da su, alhãli kuwa bã da Mun rage musu kõme ba daga aikinsu, kõwane mutum jingina ne ga abin da ya sana'anta.
____________________
* Wannan ãyã tanã nũna yadda wani ke ceton wani sabõda kusanci dõmin a ƙãra daukaka mai ceton. Sharaɗin ceton shĩ ne wanda ake ceton yanã da nãsa ĩmanin. Wanda jinginarsa ta halaka bãbu mai cetonsa. Zuriya ta haɗa uwãye da almajiran mãlami sãlihi. Suna shiga a cikin cetonsa.
____________________
* Wannan ãyã tanã nũna yadda wani ke ceton wani sabõda kusanci dõmin a ƙãra daukaka mai ceton. Sharaɗin ceton shĩ ne wanda ake ceton yanã da nãsa ĩmanin. Wanda jinginarsa ta halaka bãbu mai cetonsa. Zuriya ta haɗa uwãye da almajiran mãlami sãlihi. Suna shiga a cikin cetonsa.
آية رقم 22
ﮚﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Kuma Muka yalwata musu 'ya'yan itãce da nãma irin wanda suke marmari.
آية رقم 23
Sunã mĩƙa wa jũnansu a cikinta hinjãlan giya, wadda bãbu yãsassar magana a cikinta, kuma bãbu jin nauyin zunubi.
آية رقم 24
Kuma waɗansu samãri nã gẽwayãwa a kansu, kamar dai sũ lu'ulu'u ne wanda ke kulle.
آية رقم 25
ﯓﯔﯕﯖﯗ
ﯘ
Waɗansunsu suka fuskanta zuwa ga waɗansu, sunã tambayar jũna.
آية رقم 26
Suka ce: "Lalle mũ mun kasance a gabãnin wannan (a dũniya) a cikin iyãlanmu munã jin tsõro."
آية رقم 27
ﯡﯢﯣﯤﯥﯦ
ﯧ
"To, Allah Yã yi mana kyautar falala, kuma Yã tsare mana azãbar iskar zãfi."
آية رقم 28
"Lalle mũ mun kasance, a gãbanin haka, munã kiran sa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai kyautatãwa, Mai rahama."
آية رقم 29
To, ka tunãtar kai fa sabõda ni'imar Ubangjinka, bã bõka kake ba, kuma bã mahaukaci ba.
آية رقم 30
Shin zã su ce: "Mawãƙi ne, munã jiran, masĩfun mutuwa game da shĩ"?
آية رقم 31
ﰄﰅﰆﰇﰈﰉ
ﰊ
Ka ce: "Ku yi jira, domin nĩ ma lalle inã a cikin mãsu jira tãre da ku."
آية رقم 32
Shin, hankulansu ne ke umarin su da wannan, kõ kuwa sũ wasu mutãne ne mãsu ƙetare haddi?
آية رقم 33
Shin, cẽwa suke yi: "Shi ne ke ƙãga faɗarsa"? Ã'a ba su dai yi ĩmãni ba.
آية رقم 34
ﭣﭤﭥﭦﭧﭨ
ﭩ
Sai su zõ da wani lãbãri mai misãlinsa idan sun kasance sũmãsu gaskiya ne.
آية رقم 35
Shin, an halitta su ne bã daga kõme ba, kõ kuwa sũ ne mãsu yin halitta?
آية رقم 36
Shin, sun halitta sammai da ƙasa ne? Ã'a ba su dai yi ĩmãnin yaƙĩni ba.
آية رقم 37
Shin, taskõkin Ubangijinka, sunã a wurinsu ne? Kõ kuwa sũ ne mãsu rinjãya?
آية رقم 38
Shin, sunã da wani tsãni ne wanda suke (hawa sunã) saurãron (lãbãrin samã) a cikinsa? Sai mai saurarõnsu ya zo da wani dalĩli bayyananne.
آية رقم 39
ﮏﮐﮑﮒﮓ
ﮔ
Shin, Yanã da* 'ya'ya mãtã ne kuma kũ, kunã da ɗiya maza ne?
____________________
* Waɗansu Lãrãbawa sunãkiran Malã'ika 'ya'yan Allah mãtã, sunã kuma bauta musu dõmin su cece su daga Allah, suna yin gumãka da sũnansu.
____________________
* Waɗansu Lãrãbawa sunãkiran Malã'ika 'ya'yan Allah mãtã, sunã kuma bauta musu dõmin su cece su daga Allah, suna yin gumãka da sũnansu.
آية رقم 40
Shin, kanã tambayar su wata ijãra ne, sabõda haka suka zama mãsu jin nauyin biyan tãrar?
آية رقم 41
ﮝﮞﮟﮠﮡ
ﮢ
Shin, a wurinsu akwai ilmin gaibi, sabõda haka sunã rubũtãwa?
آية رقم 42
Shin, sunã nufin wani kaidi ne? To, waɗanda suka kãfirta sũ ne waɗanda ake yi wa kaidi.
آية رقم 43
Shin, sunã da wani abin bautãwa ne wanda bã Allah ba? Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke yi na shirki!
آية رقم 44
Kuma idan sun ga wani ɓaɓɓake daga samã yãnã fãɗuwa, sai su ce wani girgije ne, mai hauhawar jũna.
آية رقم 45
To, ka bar su, sai sun haɗu da yinin nan da za a sũmar da su a cikinsa.
آية رقم 46
Rãnar da kaidinsu bã ya wadãtar masu da kõme, kuma bã a taimakon su.
آية رقم 47
Kuma lalle, waɗannan da suka yi zãluncin, sunã da azãba (a nan dũniya) banda waccan, kuma mafi yawansu ba su sani ba.
آية رقم 48
Sai ka yi hakuri da hukuncin Ubangijinka, lalle kai fa kanã idãnunMu, kuma ka tsarkake* Ubangijinka da (tasbĩhi) game da gõde Masa a lõkacin da kake tãshi tsaye (dõmin salla kõ wani abu).
____________________
* (Ma'anar ita ce tsarkakewa kõ tasbĩhi, 'tsare sallõli, farillai, anã cewa' faɗin "Subhãnal lãhi wal Hamdu Lillãhi" a bãyan kõwane mazauni, dõmin ya zama kaffãrar wannan mazaunin.
____________________
* (Ma'anar ita ce tsarkakewa kõ tasbĩhi, 'tsare sallõli, farillai, anã cewa' faɗin "Subhãnal lãhi wal Hamdu Lillãhi" a bãyan kõwane mazauni, dõmin ya zama kaffãrar wannan mazaunin.
آية رقم 49
ﰋﰌﰍﰎﰏ
ﰐ
Kuma daga dare, sai ka tsarkake Shi (da tasbĩhin) dalõkacin jũyãwar taurãri.
تقدم القراءة