ترجمة معاني سورة الشمس باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﭜﭝ
ﭞ
As-Shams
Ina rantsuwa da rãnã da hantsinta.
آية رقم 2
ﭟﭠﭡ
ﭢ
Kuma da wata idan ya bi ta.
آية رقم 3
ﭣﭤﭥ
ﭦ
Da yini a lõkacin da ya bayyana ta.
آية رقم 4
ﭧﭨﭩ
ﭪ
Da dare a lõkacin da ya ke rufe ta.
آية رقم 5
ﭫﭬﭭ
ﭮ
Da sama da abin da ya gina ta.
آية رقم 6
ﭯﭰﭱ
ﭲ
Da ƙasã da abin da ya shimfiɗa ta.
آية رقم 7
ﭳﭴﭵ
ﭶ
Da rai da abin da ya daidaita shi.
آية رقم 8
ﭷﭸﭹ
ﭺ
Sa'an nan ya sanar da shi fãjircinsa da shiryuwarsa.
آية رقم 9
ﭻﭼﭽﭾ
ﭿ
Lalle ne wanda ya tsarkake shi (rai) ya sãmi babban rabo.
آية رقم 10
ﮀﮁﮂﮃ
ﮄ
Kuma lalle ne wanda ya turbuɗe shi (da laifi) ya tãɓe.
آية رقم 11
ﮅﮆﮇ
ﮈ
Samũdãwa sun ƙaryata (Annabinsu), dõmin girman kansu.
آية رقم 12
ﮉﮊﮋ
ﮌ
A lõkacin da mafi shaƙãwarsu ya tafi (wurin sõke rãkumar sãlihu).
آية رقم 13
Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsõratar da ku ga rãƙumar Allah da ruwan shanta!"
آية رقم 14
Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka sõke ta. Sabõda haka Ubangijinsu Ya darkãke su, sabõda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azãbar ga mai laifi da maras laifi).
آية رقم 15
ﮝﮞﮟ
ﮠ
Kuma bã ya tsõron ãƙibarta (ita halakãwar).
تقدم القراءة