ترجمة معاني سورة البلد باللغة الهوساوية من كتاب الترجمة الهوساوية

الترجمة الهوساوية

الناشر

مجمع الملك فهد

آية رقم 1
Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari* ba.
____________________
  * Allah Ya ce ba sai Ya yi rantsuwa da Makka ba, sa'an nan zã a san darajarta a lõkacinda Annabi yake a cikinta, kuma shi yana da haƙƙin zama a cikinta mahaifansa da zurriyarsa duka, ko da yake zai yi hijira sabõda fitinar kãfirai mãsu halaka dũkiyarsu kan adãwa da shi. Dã sun yi amfãni da dukiyar ga ayyukan alheri, dã yã fi musu.
آية رقم 6
Yana cẽwa "Na* halakarda dũkiya mai yawa,"
____________________
 * Nã halaka dukiya mai yawa dõmin faɗã da addĩni.
آية رقم 9
Da harshe, da leɓɓa biyu.
آية رقم 10
Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi* biyu ba?
____________________
* Hanyar alheri da ta sharri.
آية رقم 12
Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?
آية رقم 13
Ita ce fansar wuyan bãwa.
Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.
آية رقم 18
Waɗannan ne ma'abũta albarka*
____________________
 * Ko kuwa waɗanda ake bai wa takardunsu da dãma, a Lãhira.
آية رقم 19
Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci(5)
____________________
  (5) Ko kuwa waɗanda ake bai wa takardunsu da hagu, a Lãhira.
تقدم القراءة