ترجمة معاني سورة البلد باللغة الهوساوية من كتاب الترجمة الهوساوية
ﰡ
آية رقم 1
ﭽﭾﭿﮀ
ﮁ
Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari* ba.
____________________
* Allah Ya ce ba sai Ya yi rantsuwa da Makka ba, sa'an nan zã a san darajarta a lõkacinda Annabi yake a cikinta, kuma shi yana da haƙƙin zama a cikinta mahaifansa da zurriyarsa duka, ko da yake zai yi hijira sabõda fitinar kãfirai mãsu halaka dũkiyarsu kan adãwa da shi. Dã sun yi amfãni da dukiyar ga ayyukan alheri, dã yã fi musu.
____________________
* Allah Ya ce ba sai Ya yi rantsuwa da Makka ba, sa'an nan zã a san darajarta a lõkacinda Annabi yake a cikinta, kuma shi yana da haƙƙin zama a cikinta mahaifansa da zurriyarsa duka, ko da yake zai yi hijira sabõda fitinar kãfirai mãsu halaka dũkiyarsu kan adãwa da shi. Dã sun yi amfãni da dukiyar ga ayyukan alheri, dã yã fi musu.
آية رقم 2
ﮂﮃﮄﮅ
ﮆ
Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.
آية رقم 3
ﮇﮈﮉ
ﮊ
Da mahaifi da abin da ya haifa.
آية رقم 4
ﮋﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.
آية رقم 5
ﮑﮒﮓﮔﮕﮖ
ﮗ
Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?
آية رقم 6
ﮘﮙﮚﮛ
ﮜ
Yana cẽwa "Na* halakarda dũkiya mai yawa,"
____________________
* Nã halaka dukiya mai yawa dõmin faɗã da addĩni.
____________________
* Nã halaka dukiya mai yawa dõmin faɗã da addĩni.
آية رقم 7
ﮝﮞﮟﮠﮡ
ﮢ
Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?
آية رقم 8
ﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?
آية رقم 9
ﮨﮩ
ﮪ
Da harshe, da leɓɓa biyu.
آية رقم 10
ﮫﮬ
ﮭ
Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi* biyu ba?
____________________
* Hanyar alheri da ta sharri.
____________________
* Hanyar alheri da ta sharri.
آية رقم 11
ﮮﮯﮰ
ﮱ
To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?
آية رقم 12
ﯓﯔﯕﯖ
ﯗ
Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?
آية رقم 13
ﯘﯙ
ﯚ
Ita ce fansar wuyan bãwa.
آية رقم 14
ﯛﯜﯝﯞﯟﯠ
ﯡ
Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.
آية رقم 15
ﯢﯣﯤ
ﯥ
Ga marãya ma'abũcin zumunta.
آية رقم 16
ﯦﯧﯨﯩ
ﯪ
Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.
آية رقم 17
Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.
آية رقم 18
ﯵﯶﯷ
ﯸ
Waɗannan ne ma'abũta albarka*
____________________
* Ko kuwa waɗanda ake bai wa takardunsu da dãma, a Lãhira.
____________________
* Ko kuwa waɗanda ake bai wa takardunsu da dãma, a Lãhira.
آية رقم 19
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci(5)
____________________
(5) Ko kuwa waɗanda ake bai wa takardunsu da hagu, a Lãhira.
____________________
(5) Ko kuwa waɗanda ake bai wa takardunsu da hagu, a Lãhira.
آية رقم 20
ﭘﭙﭚ
ﭛ
A kansu akwai wata wuta abar kullewa.
تقدم القراءة