ترجمة معاني سورة المزّمّل باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﭑﭒ
ﭓ
Al-Muzzammil
Yã wanda ya lulluɓe!
آية رقم 2
ﭔﭕﭖﭗ
ﭘ
Ka tsayu domin yin salla a cikin dare (duka) fãce kaɗan.
آية رقم 3
ﭙﭚﭛﭜﭝ
ﭞ
Rabinsa, ko ka rage abu kaɗan daga gare shi.
آية رقم 4
ﭟﭠﭡﭢﭣﭤ
ﭥ
Ko ka ƙara kansa kuma ka kyautata karanta Alƙu'ãni, daki daki.
آية رقم 5
ﭦﭧﭨﭩﭪ
ﭫ
Lalle ne, Mũ, zã Mu jẽfa maka magana mai nauyi.
آية رقم 6
Lalle ne, tashin dare shi ne mafi tsananin natsuwa, kuma mafi daidaituwa ga magana.
آية رقم 7
ﭵﭶﭷﭸﭹﭺ
ﭻ
Lalle ne, kanã da, a cikin yini, wani tasĩhi mai tsawo.
آية رقم 8
ﭼﭽﭾﭿﮀﮁ
ﮂ
Kuma ka ambaci sũnan Ubangijinka, kuma ka yanke (ƙauna daga kowa ka koma) zuwa gare Shi, yankewa.
آية رقم 9
Shi ne Ubangijin mafitar rãnã da mafãɗarta, bãbu abin bautawa fãce Shi. Sabõda haka ka riƙe Shi wakili.
آية رقم 10
Kuma ka yi haƙuri ga abin da suke faɗã, kuma ka ƙaurace musu, ƙauracẽwa mai kyãwo.
آية رقم 11
ﮕﮖﮗﮘﮙﮚ
ﮛ
Kuma ka bar Ni da mãsu ƙaryatãwa, mawadãta, kuma ka jinkirta musu kaɗan.
آية رقم 12
ﮜﮝﮞﮟ
ﮠ
Lalle ne, a wurinMu, akwai wasu marũruwa mãsu nauyi da Jahĩm.
آية رقم 13
ﮡﮢﮣﮤﮥ
ﮦ
Da wani abinci mai mãƙara da azãba mai raɗaɗi.
آية رقم 14
Rãnar da ƙasa ke raurawa, da duwãtsu kuma duwãtsu su kasance tudun rairayi mai malãlã.
آية رقم 15
Lalle ne, Mũ. Mun aika zuwa gare ku, wani Manzo mai shaida a kanku, kamar yadda Muka aika wani Manzo zuwaga Fir'auna,
آية رقم 16
ﯝﯞﯟﯠﯡﯢ
ﯣ
Sai Fir'auna ya saɓa wa Manzon, saboda haka Muka kãma shi kãmu mai tsanani.
آية رقم 17
To, yãya, idan kun kãfirta, zã ku kãre (azabar) wani yini mai mayar da yãra (tsofaffi) mãsu hurhura.
آية رقم 18
Sama za ta tsãge a cikinsa, wa'adinsa yã kasance mai aukuwa.
آية رقم 19
Lalle ne, wannan wata tunãtarwa ce, sai dai wanda ya so, ya kãma hanyar ƙwarai zuwa ga Ubangijinsa.
آية رقم 20
Lalle ne, Ubangijinka Yã sani cẽwa, kai kana tsayuwa a kusan kashi biyu daga uku na dare, da rabinsa, da sulusinsa, tãre da wani ɓangare na waɗanda ke tãre da kai. Allah Yake iya ƙaddara dare da yini, Ya san bã zã ku iya lissafa shi ba, sabõda haka Ya karɓi tubarku sai, ku karanta abin da ya sauƙaƙa na Alƙur'ãni. Ya san wasu daga cikinku, zã su yi cĩwo, kuma wasu zã su yi tafiya cikin ƙasa suna nẽman falalar Allah da fatauci, kuma wasu zã su yi yãƙi a cikin banyar Allah. Sabõda haka ku karanta abin da ya sauƙaƙa daga gare shi, kuma ku tsai da salla kuma ku bãyar da zakka, kumaa ku bai wa Allah rance, rance mai kyãwo. Kuma abin da kuka gabatar dõmin kanku, na alhẽri, zã ku sãme shi a wurin Allah zai kasance mafifici (daga wanda kuka ajiye) kuma zai fi girma ga sakamako, kuma ku rõƙi Allah gãfara; lalle ne Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.
تقدم القراءة