ترجمة معاني سورة عبس باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

آية رقم 1

Abasa


Yã game huska kuma ya jũya bãya.
آية رقم 3

To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.
آية رقم 6

Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!
آية رقم 9

Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.
آية رقم 11

A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.
آية رقم 12

Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).
آية رقم 13

(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,
آية رقم 14

Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.
آية رقم 15

A cikin hannãyen mala'iku marubũta.
آية رقم 16

Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.
آية رقم 17

An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!
آية رقم 19

Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).
آية رقم 20

Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.
آية رقم 21

Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.
آية رقم 23

Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).
آية رقم 27

Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.
آية رقم 29

Da zaitũni da itãcen dabĩno.
آية رقم 30

Da lambuna, mãsu yawan itãce.
آية رقم 31

Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.
آية رقم 32

Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.
آية رقم 33

To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.
آية رقم 37

Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.
آية رقم 38

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.
آية رقم 39

Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.
آية رقم 40

Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.
آية رقم 42

Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).
تقدم القراءة