ترجمة معاني سورة عبس باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﭑﭒ
ﭓ
Abasa
Yã game huska kuma ya jũya bãya.
آية رقم 2
ﭔﭕﭖ
ﭗ
Sabõda makãho yã je masa.
آية رقم 3
ﭘﭙﭚﭛ
ﭜ
To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.
آية رقم 4
ﭝﭞﭟﭠ
ﭡ
Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?
آية رقم 5
ﭢﭣﭤ
ﭥ
Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.
آية رقم 6
ﭦﭧﭨ
ﭩ
Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!
آية رقم 7
ﭪﭫﭬﭭ
ﭮ
To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?
آية رقم 8
ﭯﭰﭱﭲ
ﭳ
Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.
آية رقم 9
ﭴﭵ
ﭶ
Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.
آية رقم 10
ﭷﭸﭹ
ﭺ
Kai kuma kã shagala ga barinsa!
آية رقم 11
ﭻﭼﭽ
ﭾ
A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.
آية رقم 12
ﭿﮀﮁ
ﮂ
Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).
آية رقم 13
ﮃﮄﮅ
ﮆ
(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,
آية رقم 14
ﮇﮈ
ﮉ
Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.
آية رقم 15
ﮊﮋ
ﮌ
A cikin hannãyen mala'iku marubũta.
آية رقم 16
ﮍﮎ
ﮏ
Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.
آية رقم 17
ﮐﮑﮒﮓ
ﮔ
An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!
آية رقم 18
ﮕﮖﮗﮘ
ﮙ
Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?
آية رقم 19
ﮚﮛﮜﮝ
ﮞ
Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).
آية رقم 20
ﮟﮠﮡ
ﮢ
Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.
آية رقم 21
ﮣﮤﮥ
ﮦ
Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.
آية رقم 22
ﮧﮨﮩﮪ
ﮫ
Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.
آية رقم 23
ﮬﮭﮮﮯﮰ
ﮱ
Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).
آية رقم 24
ﯓﯔﯕﯖ
ﯗ
To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.
آية رقم 25
ﯘﯙﯚﯛ
ﯜ
Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.
آية رقم 26
ﯝﯞﯟﯠ
ﯡ
Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.
آية رقم 27
ﯢﯣﯤ
ﯥ
Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.
آية رقم 28
ﯦﯧ
ﯨ
Da inabi da ciyãwa.
آية رقم 29
ﯩﯪ
ﯫ
Da zaitũni da itãcen dabĩno.
آية رقم 30
ﯬﯭ
ﯮ
Da lambuna, mãsu yawan itãce.
آية رقم 31
ﯯﯰ
ﯱ
Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.
آية رقم 32
ﯲﯳﯴ
ﯵ
Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.
آية رقم 33
ﯶﯷﯸ
ﯹ
To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.
آية رقم 34
ﯺﯻﯼﯽﯾ
ﯿ
Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.
آية رقم 35
ﰀﰁ
ﰂ
Da uwarsa da ubansa.
آية رقم 36
ﰃﰄ
ﰅ
Da mãtarsa da ɗiyansa.
آية رقم 37
ﰆﰇﰈﰉﰊﰋ
ﰌ
Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.
آية رقم 38
ﰍﰎﰏ
ﰐ
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.
آية رقم 39
ﰑﰒ
ﰓ
Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.
آية رقم 40
ﰔﰕﰖﰗ
ﰘ
Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.
آية رقم 41
ﭑﭒ
ﭓ
Baƙi zai rufe su.
آية رقم 42
ﭔﭕﭖﭗ
ﭘ
Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).
تقدم القراءة