ترجمة معاني سورة البلد باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﭽﭾﭿﮀ
ﮁ
Al-Balad
Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.
آية رقم 2
ﮂﮃﮄﮅ
ﮆ
Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.
آية رقم 3
ﮇﮈﮉ
ﮊ
Da mahaifi da abin da ya haifa.
آية رقم 4
ﮋﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.
آية رقم 5
ﮑﮒﮓﮔﮕﮖ
ﮗ
Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?
آية رقم 6
ﮘﮙﮚﮛ
ﮜ
Yana cẽwa "Na halakarda dũkiya mai yawa,"
آية رقم 7
ﮝﮞﮟﮠﮡ
ﮢ
Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?
آية رقم 8
ﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?
آية رقم 9
ﮨﮩ
ﮪ
Da harshe, da leɓɓa biyu.
آية رقم 10
ﮫﮬ
ﮭ
Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi biyu ba?
آية رقم 11
ﮮﮯﮰ
ﮱ
To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?
آية رقم 12
ﯓﯔﯕﯖ
ﯗ
Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?
آية رقم 13
ﯘﯙ
ﯚ
Ita ce fansar wuyan bãwa.
آية رقم 14
ﯛﯜﯝﯞﯟﯠ
ﯡ
Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.
آية رقم 15
ﯢﯣﯤ
ﯥ
Ga marãya ma'abũcin zumunta.
آية رقم 16
ﯦﯧﯨﯩ
ﯪ
Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.
آية رقم 17
Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.
آية رقم 18
ﯵﯶﯷ
ﯸ
Waɗannan ne ma'abũta albarka
آية رقم 19
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci
آية رقم 20
ﭘﭙﭚ
ﭛ
A kansu akwai wata wuta abar kullewa.
تقدم القراءة