ترجمة معاني سورة القيامة باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

آية رقم 1

Al-Kiyama


Bã sai Nã yi rantsuwa da Rãnar ¡iyãma ba.
آية رقم 2

Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin kansa ba.
آية رقم 5

Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.
آية رقم 7

To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).
آية رقم 8

Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).
آية رقم 12

zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.
آية رقم 13

Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.
آية رقم 15

Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).
آية رقم 16

Kada ka mõtsar da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).
آية رقم 17

Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.
آية رقم 19

sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.
آية رقم 20

A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.
آية رقم 21

Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).
آية رقم 22

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.
آية رقم 24

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.
آية رقم 29

Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.
آية رقم 30

Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa take.
آية رقم 32

Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!
آية رقم 34

Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.
آية رقم 35

Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.
آية رقم 36

Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?
آية رقم 38

Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;
تقدم القراءة