ترجمة معاني سورة الإنشقاق باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﭣﭤﭥ
ﭦ
Al-Inshikak
Idan sama ta kẽce,
آية رقم 2
ﭧﭨﭩ
ﭪ
Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,
آية رقم 3
ﭫﭬﭭ
ﭮ
Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,
آية رقم 4
ﭯﭰﭱﭲ
ﭳ
Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.
آية رقم 5
ﭴﭵﭶ
ﭷ
Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,
آية رقم 6
Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.
آية رقم 7
ﮁﮂﮃﮄﮅ
ﮆ
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.
آية رقم 8
ﮇﮈﮉﮊ
ﮋ
To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.
آية رقم 9
ﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.
آية رقم 10
ﮑﮒﮓﮔﮕﮖ
ﮗ
Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.
آية رقم 11
ﮘﮙﮚ
ﮛ
To, zã shi dinga kiran halaka!
آية رقم 12
ﮜﮝ
ﮞ
Kuma ya shiga sa'ĩr.
آية رقم 13
ﮟﮠﮡﮢﮣ
ﮤ
Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.
آية رقم 14
ﮥﮦﮧﮨﮩ
ﮪ
Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.
آية رقم 15
Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.
آية رقم 16
ﯔﯕﯖ
ﯗ
To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.
آية رقم 17
ﯘﯙﯚ
ﯛ
Da dare, da abin da ya ƙunsa.
آية رقم 18
ﯜﯝﯞ
ﯟ
Da watã idan (haskensa) ya cika.
آية رقم 19
ﯠﯡﯢﯣ
ﯤ
Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.
آية رقم 20
ﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?
آية رقم 21
Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?
آية رقم 22
ﯲﯳﯴﯵ
ﯶ
Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.
آية رقم 23
ﯷﯸﯹﯺ
ﯻ
Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.
آية رقم 24
ﯼﯽﯾ
ﯿ
Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.
آية رقم 25
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.
تقدم القراءة