ترجمة معاني سورة الإنشقاق باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

آية رقم 2

Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,
آية رقم 4

Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.
آية رقم 5

Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,
آية رقم 6

Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.
آية رقم 9

Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.
آية رقم 13

Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.
آية رقم 22

Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.
آية رقم 23

Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.
آية رقم 24

Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.
تقدم القراءة