ترجمة معاني سورة البروج باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﭛﭜﭝ
ﭞ
Al-Buruj
Inã rantsuwa da sama mai taurãrin lissafin shekara.
آية رقم 2
ﭟﭠ
ﭡ
Da yinin da aka yi alkawarin zuwansa,
آية رقم 3
ﭢﭣ
ﭤ
Da yini mai shaidu, da yini da ake halarta a cikinsa
آية رقم 4
ﭥﭦﭧ
ﭨ
An la'ani mutãnen rãmi.
آية رقم 5
ﭩﭪﭫ
ﭬ
Wato wuta wadda aka hura.
آية رقم 6
ﭭﭮﭯﭰ
ﭱ
A lõkacin da suke a kan (gefen) ta a zazzaune.
آية رقم 7
ﭲﭳﭴﭵﭶﭷ
ﭸ
Alhãli sũ, bisa ga abin da suke aikatãwa ga mũminai, sunã halarce.
آية رقم 8
Kuma ba su tuhumce su ba, fãce kawai domin sun yi ĩmãni da Allah Mabuwãyi, wanda ake gõdewa.
آية رقم 9
Wanda Yake shi ne da mulkin sammai da ƙasa, kuma Allah a kan kõme halarce Yake.
آية رقم 10
Lalle ne waɗanda suka fitini mũminai maza da mũminai mãta, sa'an nan ba su tũba ba to, sunã da azãbar Jahannama, kuma sunã da azãbar gõbara.
آية رقم 11
Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da gidãjen Aljanna, ƙoramu na gudãna daga ƙarƙashin gidãjen. Wancan abu fa shi ne rabo babba.
آية رقم 12
ﮮﮯﮰﮱ
ﯓ
Lalle ne damƙar Ubangijinka mai tsanani ce ƙwarai.
آية رقم 13
ﯔﯕﯖﯗ
ﯘ
Lalle ne Shĩ, Shi ne Mai ƙãga halitta, kuma Ya mayar da ita (bãyan mutuwa).
آية رقم 14
ﯙﯚﯛ
ﯜ
Kuma Shi ne Mai gãfara, Mai bayyana sõyayya.
آية رقم 15
ﯝﯞﯟ
ﯠ
Mai Al'arshi mai girma
آية رقم 16
ﯡﯢﯣ
ﯤ
Mai aikatãwa ga abin da Yake nufi.
آية رقم 17
ﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
Ko lãbãrin rundanõni yã zo maka.
آية رقم 18
ﯪﯫ
ﯬ
Fir'auna da samũdãwa?
آية رقم 19
ﯭﯮﯯﯰﯱ
ﯲ
Ã'aha! waɗanda suka kãfirta sunã cikin ƙaryatãwa.
آية رقم 20
ﯳﯴﯵﯶ
ﯷ
Alhãli, Allah daga bãyansu, Mai kẽwaye su ne (da saninSa).
آية رقم 21
ﯸﯹﯺﯻ
ﯼ
Ã'aha! Shi Alƙur'ãni ne mai girma.
آية رقم 22
ﯽﯾﯿ
ﰀ
A cikin Allo tsararre.
تقدم القراءة