ترجمة معاني سورة المعارج باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﮮﮯﮰﮱ
ﯓ
Al-Ma'arij
Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.
آية رقم 2
ﯔﯕﯖﯗ
ﯘ
Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.
آية رقم 3
ﯙﯚﯛﯜ
ﯝ
Daga Allah Mai matãkala.
آية رقم 4
Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.
آية رقم 5
ﯪﯫﯬ
ﯭ
Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.
آية رقم 6
ﯮﯯﯰ
ﯱ
Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.
آية رقم 7
ﯲﯳ
ﯴ
Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.
آية رقم 8
ﯵﯶﯷﯸ
ﯹ
Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.
آية رقم 9
ﯺﯻﯼ
ﯽ
Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.
آية رقم 10
ﯾﯿﰀﰁ
ﰂ
Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.
آية رقم 11
Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,
آية رقم 12
ﭜﭝ
ﭞ
Da matarsa da ɗan'uwansa.
آية رقم 13
ﭟﭠﭡ
ﭢ
Da danginsa, mãsu tattarã shi.
آية رقم 14
ﭣﭤﭥﭦﭧﭨ
ﭩ
Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.
آية رقم 15
ﭪﭫﭬﭭ
ﭮ
A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,
آية رقم 16
ﭯﭰ
ﭱ
Mai twãle fãtar goshi.
آية رقم 17
ﭲﭳﭴﭵ
ﭶ
Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.
آية رقم 18
ﭷﭸ
ﭹ
Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.
آية رقم 19
ﭺﭻﭼﭽﭾ
ﭿ
Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.
آية رقم 20
ﮀﮁﮂﮃ
ﮄ
Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.
آية رقم 21
ﮅﮆﮇﮈ
ﮉ
Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.
آية رقم 22
ﮊﮋ
ﮌ
Sai mãsu yin salla,
آية رقم 23
ﮍﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.
آية رقم 24
ﮓﮔﮕﮖﮗ
ﮘ
Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.
آية رقم 25
ﮙﮚ
ﮛ
Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.
آية رقم 26
ﮜﮝﮞﮟ
ﮠ
Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.
آية رقم 27
ﮡﮢﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.
آية رقم 28
ﮨﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.
آية رقم 29
ﮮﮯﮰﮱ
ﯓ
Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.
آية رقم 30
Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.
آية رقم 31
To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.
آية رقم 32
ﯧﯨﯩﯪﯫ
ﯬ
Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.
آية رقم 33
ﯭﯮﯯﯰ
ﯱ
Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.
آية رقم 34
ﯲﯳﯴﯵﯶ
ﯷ
Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.
آية رقم 35
ﯸﯹﯺﯻ
ﯼ
Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne
آية رقم 36
ﯽﯾﯿﰀﰁ
ﰂ
Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).
آية رقم 37
ﰃﰄﰅﰆﰇ
ﰈ
Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!
آية رقم 38
Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?
آية رقم 39
ﰒﰓﰔﰕﰖﰗ
ﰘ
A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.
آية رقم 40
Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.
آية رقم 41
Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.
آية رقم 42
Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).
آية رقم 43
Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.
آية رقم 44
Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)
تقدم القراءة