ترجمة معاني سورة الصافات باللغة الهوساوية من كتاب الترجمة الهوساوية
ﰡ
آية رقم 1
ﭑﭒ
ﭓ
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
آية رقم 2
ﭔﭕ
ﭖ
Sa'an nan mãsu yin tsãwa* dõmin gargaɗi.
____________________
* Mãsu tsãwa, sũ ne Malamai mãsu sãmun ilmin wa'azi daga Annabãwa waɗanda ke karãtun abin tunãwa daga Allah Ubangijin sammai da ƙasa, Mai bãyar da haske ga rãnã, Mai haskaka taurari mãsu ƙãwãtar da samã kuma su tsare ta daga shaiɗanu. An siffanta rãnã da Annabãwa, Malamai da taurãri, ilmi da haske da sababin ƙawa da shiryarwa da kõrar mãsu ɓarna.
____________________
* Mãsu tsãwa, sũ ne Malamai mãsu sãmun ilmin wa'azi daga Annabãwa waɗanda ke karãtun abin tunãwa daga Allah Ubangijin sammai da ƙasa, Mai bãyar da haske ga rãnã, Mai haskaka taurari mãsu ƙãwãtar da samã kuma su tsare ta daga shaiɗanu. An siffanta rãnã da Annabãwa, Malamai da taurãri, ilmi da haske da sababin ƙawa da shiryarwa da kõrar mãsu ɓarna.
آية رقم 3
ﭗﭘ
ﭙ
Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
آية رقم 4
ﭚﭛﭜ
ﭝ
Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.
آية رقم 5
Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.
آية رقم 6
ﭦﭧﭨﭩﭪﭫ
ﭬ
Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.
آية رقم 7
ﭭﭮﭯﭰﭱ
ﭲ
Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.
آية رقم 8
Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.
آية رقم 9
ﭽﭾﭿﮀﮁ
ﮂ
Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
آية رقم 10
Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.
آية رقم 11
Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.
آية رقم 12
ﮙﮚﮛ
ﮜ
Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
آية رقم 13
ﮝﮞﮟﮠ
ﮡ
Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.
آية رقم 14
ﮢﮣﮤﮥ
ﮦ
Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.
آية رقم 15
ﮧﮨﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."
آية رقم 16
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
آية رقم 17
ﯗﯘ
ﯙ
"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"
آية رقم 18
ﯚﯛﯜﯝ
ﯞ
Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."
آية رقم 19
Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.
آية رقم 20
ﯧﯨﯩﯪﯫ
ﯬ
Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."
آية رقم 21
Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.
آية رقم 22
Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.
آية رقم 23
Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.
آية رقم 24
ﰆﰇﰈﰉ
ﰊ
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
آية رقم 25
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?
آية رقم 26
ﭖﭗﭘﭙ
ﭚ
Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.
آية رقم 27
ﭛﭜﭝﭞﭟ
ﭠ
Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.
آية رقم 28
ﭡﭢﭣﭤﭥﭦ
ﭧ
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
آية رقم 29
ﭨﭩﭪﭫﭬ
ﭭ
Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.
آية رقم 30
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."
آية رقم 31
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
آية رقم 32
ﮂﮃﮄﮅ
ﮆ
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
آية رقم 33
ﮇﮈﮉﮊﮋ
ﮌ
To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.
آية رقم 34
ﮍﮎﮏﮐ
ﮑ
Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
آية رقم 35
Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.
آية رقم 36
ﮝﮞﮟﮠﮡﮢ
ﮣ
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
آية رقم 37
ﮤﮥﮦﮧﮨ
ﮩ
Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
آية رقم 38
ﮪﮫﮬﮭ
ﮮ
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
آية رقم 39
ﮯﮰﮱﯓﯔﯕ
ﯖ
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
آية رقم 40
ﯗﯘﯙﯚ
ﯛ
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
آية رقم 41
ﯜﯝﯞﯟ
ﯠ
Waɗannan sunã da abinci sananne.
آية رقم 42
ﯡﯢﯣ
ﯤ
'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
آية رقم 43
ﯥﯦﯧ
ﯨ
A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.
آية رقم 44
ﯩﯪﯫ
ﯬ
A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.
آية رقم 45
ﯭﯮﯯﯰﯱ
ﯲ
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
آية رقم 46
ﯳﯴﯵ
ﯶ
Farã mai dãɗi ga mashãyan.
آية رقم 47
A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,
آية رقم 48
ﯿﰀﰁﰂ
ﰃ
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
آية رقم 49
ﰄﰅﰆ
ﰇ
Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.
آية رقم 50
ﰈﰉﰊﰋﰌ
ﰍ
Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.
آية رقم 51
Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."
آية رقم 52
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
آية رقم 53
"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
آية رقم 54
ﭞﭟﭠﭡ
ﭢ
(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
آية رقم 55
ﭣﭤﭥﭦﭧ
ﭨ
Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.
آية رقم 56
ﭩﭪﭫﭬﭭ
ﭮ
Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
آية رقم 57
ﭯﭰﭱﭲﭳﭴ
ﭵ
"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
آية رقم 58
ﭶﭷﭸ
ﭹ
"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."
آية رقم 59
ﭺﭻﭼﭽﭾﭿ
ﮀ
"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"
آية رقم 60
ﮁﮂﮃﮄﮅ
ﮆ
Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.
آية رقم 61
ﮇﮈﮉﮊ
ﮋ
Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.
آية رقم 62
ﮌﮍﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?
آية رقم 63
ﮓﮔﮕﮖ
ﮗ
Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.
آية رقم 64
ﮘﮙﮚﮛﮜﮝ
ﮞ
Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.
آية رقم 65
ﮟﮠﮡﮢ
ﮣ
Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.
آية رقم 66
ﮤﮥﮦﮧﮨﮩ
ﮪ
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.
آية رقم 67
Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.
آية رقم 68
ﯔﯕﯖﯗﯘ
ﯙ
Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.
آية رقم 69
ﯚﯛﯜﯝ
ﯞ
Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.
آية رقم 70
ﯟﯠﯡﯢ
ﯣ
Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.
آية رقم 71
ﯤﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
آية رقم 72
ﯪﯫﯬﯭ
ﯮ
Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.
آية رقم 73
ﯯﯰﯱﯲﯳ
ﯴ
Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
آية رقم 74
ﯵﯶﯷﯸ
ﯹ
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
آية رقم 75
ﯺﯻﯼﯽﯾ
ﯿ
Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
آية رقم 76
ﰀﰁﰂﰃﰄ
ﰅ
Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.
آية رقم 77
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.
آية رقم 78
ﭖﭗﭘﭙ
ﭚ
Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.
آية رقم 79
ﭛﭜﭝﭞﭟ
ﭠ
Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.
آية رقم 80
ﭡﭢﭣﭤ
ﭥ
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
آية رقم 81
ﭦﭧﭨﭩ
ﭪ
Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.
آية رقم 82
ﭫﭬﭭ
ﭮ
Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.
آية رقم 83
ﭯﭰﭱﭲﭳ
ﭴ
Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.
آية رقم 84
ﭵﭶﭷﭸﭹ
ﭺ
A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.
آية رقم 85
ﭻﭼﭽﭾﭿﮀ
ﮁ
A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"
آية رقم 86
ﮂﮃﮄﮅﮆ
ﮇ
"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
آية رقم 87
ﮈﮉﮊﮋ
ﮌ
"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"
آية رقم 88
ﮍﮎﮏﮐ
ﮑ
Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
آية رقم 89
ﮒﮓﮔ
ﮕ
Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
آية رقم 90
ﮖﮗﮘ
ﮙ
Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
آية رقم 91
ﮚﮛﮜﮝﮞﮟ
ﮠ
Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?
آية رقم 92
ﮡﮢﮣﮤ
ﮥ
"Me ya sãme ku, bã ku magana?"
آية رقم 93
ﮦﮧﮨﮩ
ﮪ
Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.
آية رقم 94
ﮫﮬﮭ
ﮮ
Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
آية رقم 95
ﮯﮰﮱﯓ
ﯔ
Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,
آية رقم 96
ﯕﯖﯗﯘ
ﯙ
"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
آية رقم 97
Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."
آية رقم 98
ﯢﯣﯤﯥﯦ
ﯧ
Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.
آية رقم 99
ﯨﯩﯪﯫﯬﯭ
ﯮ
Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."
آية رقم 100
ﯯﯰﯱﯲﯳ
ﯴ
"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
آية رقم 101
ﯵﯶﯷ
ﯸ
Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro *mai haƙuri.
____________________
* Yãron da aka yi bushãra da shi a nan, shĩ ne Ismã'ĩla' sabõda abin da yake tafe a gaba wanda ya shãfi Is'hãƙa da sũnansa a bayyane yã nũna a nan bã shi ba ne. Watau Ismã'ĩla kawai ne.
____________________
* Yãron da aka yi bushãra da shi a nan, shĩ ne Ismã'ĩla' sabõda abin da yake tafe a gaba wanda ya shãfi Is'hãƙa da sũnansa a bayyane yã nũna a nan bã shi ba ne. Watau Ismã'ĩla kawai ne.
آية رقم 102
To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."
آية رقم 103
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Yayin da suka mika wuya sai muka fansheshi da Rago
آية رقم 104
ﭖﭗﭘ
ﭙ
Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"
آية رقم 105
"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
آية رقم 106
ﭣﭤﭥﭦﭧ
ﭨ
Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.
آية رقم 107
ﭩﭪﭫ
ﭬ
Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
آية رقم 108
ﭭﭮﭯﭰ
ﭱ
Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.
آية رقم 109
ﭲﭳﭴ
ﭵ
Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.
آية رقم 110
ﭶﭷﭸ
ﭹ
Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
آية رقم 111
ﭺﭻﭼﭽ
ﭾ
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
آية رقم 112
ﭿﮀﮁﮂﮃ
ﮄ
Kuma Muka yi masa bushãra* Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
____________________
* Wannan sãbuwar bushãra da Is'hãƙa tanã nũna cewa bã shĩ ne wanda kissar yankã ta shãfa ba sabõda haka Isma'ĩla dai ne tabbas, mai ƙissar yankã. Sabõda haka Allah Ya sanya shi wata al'umma dabam' dõmin a sãka masa, sa'an nan aka sãkawa Ibrãhĩm da Is'hãƙa dõmin ya zama wata al'umma ta dabam,.
____________________
* Wannan sãbuwar bushãra da Is'hãƙa tanã nũna cewa bã shĩ ne wanda kissar yankã ta shãfa ba sabõda haka Isma'ĩla dai ne tabbas, mai ƙissar yankã. Sabõda haka Allah Ya sanya shi wata al'umma dabam' dõmin a sãka masa, sa'an nan aka sãkawa Ibrãhĩm da Is'hãƙa dõmin ya zama wata al'umma ta dabam,.
آية رقم 113
Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).
آية رقم 114
ﮑﮒﮓﮔﮕ
ﮖ
Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.
آية رقم 115
ﮗﮘﮙﮚﮛ
ﮜ
Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.
آية رقم 116
ﮝﮞﮟﮠ
ﮡ
Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
آية رقم 117
ﮢﮣﮤ
ﮥ
Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
آية رقم 118
ﮦﮧﮨ
ﮩ
Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.
آية رقم 119
ﮪﮫﮬﮭ
ﮮ
Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.
آية رقم 120
ﮯﮰﮱﯓ
ﯔ
Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.
آية رقم 121
ﯕﯖﯗﯘ
ﯙ
Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
آية رقم 122
ﯚﯛﯜﯝ
ﯞ
Lalle, sunã daga bãyinMu mũminai.
آية رقم 123
ﯟﯠﯡﯢ
ﯣ
Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
آية رقم 124
ﯤﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"
آية رقم 125
ﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"
آية رقم 126
ﯰﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
"Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"
آية رقم 127
ﭑﭒﭓ
ﭔ
Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).
آية رقم 128
ﭕﭖﭗﭘ
ﭙ
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
آية رقم 129
ﭚﭛﭜﭝ
ﭞ
Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.
آية رقم 130
ﭟﭠﭡﭢ
ﭣ
Aminci ya tabbata ga Ilyãs.
آية رقم 131
ﭤﭥﭦﭧ
ﭨ
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
آية رقم 132
ﭩﭪﭫﭬ
ﭭ
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
آية رقم 133
ﭮﭯﭰﭱ
ﭲ
Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
آية رقم 134
ﭳﭴﭵﭶ
ﭷ
A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.
آية رقم 135
ﭸﭹﭺﭻ
ﭼ
Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).
آية رقم 136
ﭽﭾﭿ
ﮀ
Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.
آية رقم 137
ﮁﮂﮃﮄ
ﮅ
Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.
آية رقم 138
ﮆﮇﮈﮉ
ﮊ
Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?
آية رقم 139
ﮋﮌﮍﮎ
ﮏ
Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
آية رقم 140
ﮐﮑﮒﮓﮔ
ﮕ
A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.
آية رقم 141
ﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.
آية رقم 142
ﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
آية رقم 143
ﮠﮡﮢﮣﮤ
ﮥ
To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,
آية رقم 144
ﮦﮧﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.
آية رقم 145
ﮭﮮﮯﮰﮱ
ﯓ
Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.
آية رقم 146
ﯔﯕﯖﯗﯘ
ﯙ
Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.
آية رقم 147
ﯚﯛﯜﯝﯞﯟ
ﯠ
Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).
آية رقم 148
ﯡﯢﯣﯤ
ﯥ
Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.
آية رقم 149
ﯦﯧﯨﯩﯪ
ﯫ
Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"
آية رقم 150
ﯬﯭﯮﯯﯰﯱ
ﯲ
Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?
آية رقم 151
ﯳﯴﯵﯶﯷ
ﯸ
To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.
آية رقم 152
ﯹﯺﯻﯼ
ﯽ
"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.
آية رقم 153
ﯾﯿﰀﰁ
ﰂ
Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?
آية رقم 154
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?
آية رقم 155
ﭖﭗ
ﭘ
Shin, bã ku tunãni?
آية رقم 156
ﭙﭚﭛﭜ
ﭝ
Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?
آية رقم 157
ﭞﭟﭠﭡﭢ
ﭣ
To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.
آية رقم 158
Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
آية رقم 159
ﭰﭱﭲﭳ
ﭴ
Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
آية رقم 160
ﭵﭶﭷﭸ
ﭹ
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
آية رقم 161
ﭺﭻﭼ
ﭽ
To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,
آية رقم 162
ﭾﭿﮀﮁ
ﮂ
Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.
آية رقم 163
ﮃﮄﮅﮆﮇ
ﮈ
Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.
آية رقم 164
ﮉﮊﮋﮌﮍﮎ
ﮏ
"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu,* fãce yanã da matsayi sananne."
____________________
* Malã'iku da sauran halitta duka kõwa yã san matsayinsa na bauta ga Allah wanda ba Ya da dã ko diya, kuma ba Ya da dangantaka da kõwa.
____________________
* Malã'iku da sauran halitta duka kõwa yã san matsayinsa na bauta ga Allah wanda ba Ya da dã ko diya, kuma ba Ya da dangantaka da kõwa.
آية رقم 165
ﮐﮑﮒ
ﮓ
"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
آية رقم 166
ﮔﮕﮖ
ﮗ
"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
آية رقم 167
ﮘﮙﮚ
ﮛ
Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,
آية رقم 168
ﮜﮝﮞﮟﮠﮡ
ﮢ
"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."
آية رقم 169
ﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
آية رقم 170
ﮨﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.
آية رقم 171
ﮮﮯﮰﮱﯓ
ﯔ
Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.
آية رقم 172
ﯕﯖﯗ
ﯘ
Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.
آية رقم 173
ﯙﯚﯛﯜ
ﯝ
Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.
آية رقم 174
ﯞﯟﯠﯡ
ﯢ
Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.
آية رقم 175
ﯣﯤﯥ
ﯦ
Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.*
____________________
* Wannan ƙãrin bayãni ne ga abin da sũrar ke karantarwa na cewa Annabãwa sũ ne kamar rãna mai haske na asali. Mãlamai kamar taurãri suke mãsu sãmun haske daga rana su wãtsa ga dũniya kuma su kõre ɓarna. Aya ta l79 da ke tafe karfafawa ce ga ma'anar wannan.
____________________
* Wannan ƙãrin bayãni ne ga abin da sũrar ke karantarwa na cewa Annabãwa sũ ne kamar rãna mai haske na asali. Mãlamai kamar taurãri suke mãsu sãmun haske daga rana su wãtsa ga dũniya kuma su kõre ɓarna. Aya ta l79 da ke tafe karfafawa ce ga ma'anar wannan.
آية رقم 176
ﯧﯨ
ﯩ
Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?
آية رقم 177
ﯪﯫﯬﯭﯮﯯ
ﯰ
To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
آية رقم 178
ﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.
آية رقم 179
ﯶﯷﯸ
ﯹ
Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.
آية رقم 180
ﯺﯻﯼﯽﯾﯿ
ﰀ
Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.
آية رقم 181
ﰁﰂﰃ
ﰄ
Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.
آية رقم 182
ﰅﰆﰇﰈ
ﰉ
Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.
تقدم القراءة