ترجمة معاني سورة الصافات باللغة الهوساوية من كتاب الترجمة الهوساوية

الترجمة الهوساوية

الناشر

مجمع الملك فهد

آية رقم 1
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
آية رقم 2
Sa'an nan mãsu yin tsãwa* dõmin gargaɗi.
____________________
 * Mãsu tsãwa, sũ ne Malamai mãsu sãmun ilmin wa'azi daga Annabãwa waɗanda ke karãtun abin tunãwa daga Allah Ubangijin sammai da ƙasa, Mai bãyar da haske ga rãnã, Mai haskaka taurari mãsu ƙãwãtar da samã kuma su tsare ta daga shaiɗanu. An siffanta rãnã da Annabãwa, Malamai da taurãri, ilmi da haske da sababin ƙawa da shiryarwa da kõrar mãsu ɓarna.
آية رقم 3
Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
آية رقم 4
Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.
آية رقم 5
Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.
آية رقم 12
Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
آية رقم 16
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
آية رقم 17
"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"
آية رقم 24
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
آية رقم 28
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
آية رقم 31
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
آية رقم 32
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
آية رقم 34
Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
آية رقم 36
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
آية رقم 38
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
آية رقم 39
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
آية رقم 42
'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
آية رقم 44
A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.
آية رقم 45
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
آية رقم 48
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
آية رقم 51
Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."
آية رقم 52
Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
آية رقم 53
"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
آية رقم 54
(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
آية رقم 56
Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
آية رقم 57
"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
آية رقم 58
"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."
آية رقم 61
Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.
آية رقم 66
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.
آية رقم 70
Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.
آية رقم 71
Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
آية رقم 72
Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.
آية رقم 73
Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
آية رقم 75
Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
آية رقم 78
Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.
آية رقم 80
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
آية رقم 82
Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.
آية رقم 86
"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
آية رقم 87
"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"
آية رقم 88
Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
آية رقم 89
Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
آية رقم 90
Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
آية رقم 91
Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?
آية رقم 94
Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
آية رقم 96
"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
آية رقم 98
Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.
آية رقم 99
Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."
آية رقم 100
"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
آية رقم 101
Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro *mai haƙuri.
____________________
  * Yãron da aka yi bushãra da shi a nan, shĩ ne Ismã'ĩla' sabõda abin da yake tafe a gaba wanda ya shãfi Is'hãƙa da sũnansa a bayyane yã nũna a nan bã shi ba ne. Watau Ismã'ĩla kawai ne.
آية رقم 103
Yayin da suka mika wuya sai muka fansheshi da Rago
آية رقم 104
Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"
آية رقم 107
Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
آية رقم 108
Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.
آية رقم 110
Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
آية رقم 112
Kuma Muka yi masa bushãra* Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
____________________
   * Wannan sãbuwar bushãra da Is'hãƙa tanã nũna cewa bã shĩ ne wanda kissar yankã ta shãfa ba sabõda haka Isma'ĩla dai ne tabbas, mai ƙissar yankã. Sabõda haka Allah Ya sanya shi wata al'umma dabam' dõmin a sãka masa, sa'an nan aka sãkawa Ibrãhĩm da Is'hãƙa dõmin ya zama wata al'umma ta dabam,.
Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).
آية رقم 115
Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.
آية رقم 116
Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
آية رقم 117
Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
آية رقم 118
Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.
آية رقم 119
Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.
آية رقم 121
Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
آية رقم 123
Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
آية رقم 124
A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"
آية رقم 125
"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"
آية رقم 127
Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).
آية رقم 129
Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.
آية رقم 131
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
آية رقم 133
Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
آية رقم 134
A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.
آية رقم 135
Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).
آية رقم 136
Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.
آية رقم 137
Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.
آية رقم 139
Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
آية رقم 140
A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.
آية رقم 141
Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.
آية رقم 142
Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
آية رقم 144
Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.
آية رقم 145
Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.
آية رقم 147
Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).
آية رقم 148
Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.
آية رقم 149
Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"
آية رقم 152
"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.
آية رقم 153
Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?
آية رقم 154
Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?
Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
آية رقم 159
Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
آية رقم 161
To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,
آية رقم 164
"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu,* fãce yanã da matsayi sananne."
____________________
  * Malã'iku da sauran halitta duka kõwa yã san matsayinsa na bauta ga Allah wanda ba Ya da dã ko diya, kuma ba Ya da dangantaka da kõwa. 
آية رقم 165
"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
آية رقم 166
"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
آية رقم 167
Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,
آية رقم 169
"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
آية رقم 171
Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.
آية رقم 172
Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.
آية رقم 173
Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.
آية رقم 174
Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.
آية رقم 175
Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.*
____________________
* Wannan ƙãrin bayãni ne ga abin da sũrar ke karantarwa na cewa Annabãwa sũ ne kamar rãna mai haske na asali. Mãlamai kamar taurãri suke mãsu sãmun haske daga rana su wãtsa ga dũniya kuma su kõre ɓarna. Aya ta l79 da ke tafe karfafawa ce ga ma'anar wannan.
آية رقم 176
Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?
آية رقم 177
To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
آية رقم 179
Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.
آية رقم 180
Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.
آية رقم 182
Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.
تقدم القراءة