ترجمة معاني سورة الحاقة باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﮯ
ﮰ
Al-Hakkah
Kiran gaskiya!
آية رقم 2
ﮱﯓ
ﯔ
Mẽne ne kiran gaskiya?
آية رقم 3
ﯕﯖﯗﯘ
ﯙ
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?
آية رقم 4
ﯚﯛﯜﯝ
ﯞ
Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!
آية رقم 5
ﯟﯠﯡﯢ
ﯣ
To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.
آية رقم 6
ﯤﯥﯦﯧﯨﯩ
ﯪ
Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.
آية رقم 7
(Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.
آية رقم 8
ﯼﯽﯾﯿﰀ
ﰁ
To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?
آية رقم 9
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.
آية رقم 10
ﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
ﭞ
Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).
آية رقم 11
Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.
آية رقم 12
ﭧﭨﭩﭪﭫﭬ
ﭭ
Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).
آية رقم 13
ﭮﭯﭰﭱﭲﭳ
ﭴ
To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.
آية رقم 14
ﭵﭶﭷﭸﭹﭺ
ﭻ
Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.
آية رقم 15
ﭼﭽﭾ
ﭿ
A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.
آية رقم 16
ﮀﮁﮂﮃﮄ
ﮅ
Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.
آية رقم 17
Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.
آية رقم 18
ﮑﮒﮓﮔﮕﮖ
ﮗ
A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.
آية رقم 19
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."
آية رقم 20
ﮢﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."
آية رقم 21
ﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.
آية رقم 22
ﮭﮮﮯ
ﮰ
A cikin Aljanna maɗaukakiya.
آية رقم 23
ﮱﯓ
ﯔ
Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),
آية رقم 24
(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."
آية رقم 25
Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"
آية رقم 26
ﯩﯪﯫﯬ
ﯭ
"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"
آية رقم 27
ﯮﯯﯰ
ﯱ
"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!
آية رقم 28
ﯲﯳﯴﯵﯶ
ﯷ
"Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"
آية رقم 29
ﯸﯹﯺ
ﯻ
"Ĩkona ya ɓace mini!"
آية رقم 30
ﯼﯽ
ﯾ
(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."
آية رقم 31
ﯿﰀﰁ
ﰂ
"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."
آية رقم 32
"Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."
آية رقم 33
ﰋﰌﰍﰎﰏﰐ
ﰑ
"Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"
آية رقم 34
ﰒﰓﰔﰕﰖ
ﰗ
"Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"
آية رقم 35
ﰘﰙﰚﰛﰜ
ﰝ
"Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."
آية رقم 36
ﭑﭒﭓﭔﭕ
ﭖ
"Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."
آية رقم 37
ﭗﭘﭙﭚ
ﭛ
"Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."
آية رقم 38
ﭜﭝﭞﭟ
ﭠ
To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,
آية رقم 39
ﭡﭢﭣ
ﭤ
Da abin da bã ku iya gani.
آية رقم 40
ﭥﭦﭧﭨ
ﭩ
Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.
آية رقم 41
Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.
آية رقم 42
Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.
آية رقم 43
ﭻﭼﭽﭾ
ﭿ
Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.
آية رقم 44
ﮀﮁﮂﮃﮄ
ﮅ
Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.
آية رقم 45
ﮆﮇﮈ
ﮉ
Dã Mun kãma shi da dãma.
آية رقم 46
ﮊﮋﮌﮍ
ﮎ
sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.
آية رقم 47
ﮏﮐﮑﮒﮓﮔ
ﮕ
Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.
آية رقم 48
ﮖﮗﮘ
ﮙ
Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.
آية رقم 49
ﮚﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.
آية رقم 50
ﮠﮡﮢﮣ
ﮤ
Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.
آية رقم 51
ﮥﮦﮧ
ﮨ
Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.
آية رقم 52
ﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.
تقدم القراءة