ترجمة معاني سورة الحاقة باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

آية رقم 1

Al-Hakkah


Kiran gaskiya!
آية رقم 3

Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?
آية رقم 4

Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!
آية رقم 5

To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.
آية رقم 6

Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.
آية رقم 9

Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.
آية رقم 10

Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).
آية رقم 11

Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.
آية رقم 12

Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).

Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.
آية رقم 18

A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.

To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."
آية رقم 20

"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."
آية رقم 21

Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.
آية رقم 23

Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),
آية رقم 24

(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."
آية رقم 26

"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"
آية رقم 27

"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!
آية رقم 30

(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."
آية رقم 31

"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."
آية رقم 38

To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,
آية رقم 40

Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.
آية رقم 44

Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.
آية رقم 48

Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.
آية رقم 49

Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.
آية رقم 50

Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.
آية رقم 51

Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.
آية رقم 52

Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.
تقدم القراءة