ترجمة معاني سورة الشعراء باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

آية رقم 1

As-Shu'ara


¦. S̃. M̃.
آية رقم 3

Tsammãninka kai mai halakar da ranka ne, dõmin ba su kasance mũminai ba!
آية رقم 6

To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.
آية رقم 9

Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.
آية رقم 13

"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.
آية رقم 14

"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."
آية رقم 16

"Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne."

"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."
آية رقم 29

Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."
آية رقم 30

Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"
آية رقم 34

(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!
آية رقم 36

Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."
آية رقم 37

"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."

Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."
آية رقم 46

Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.
آية رقم 54

"Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan."
آية رقم 55

"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."
آية رقم 56

"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."
آية رقم 60

Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.
آية رقم 61

Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."
آية رقم 64

Kuma Muka kusantar da waɗansu mutãne a can.
آية رقم 65

Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.
آية رقم 66

Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.
آية رقم 68

Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.
آية رقم 71

Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."
آية رقم 73

"Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?"
آية رقم 75

Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?"
آية رقم 78

"Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni."
آية رقم 79

"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."
آية رقم 80

"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."
آية رقم 81

"Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni."
آية رقم 87

"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."
آية رقم 90

Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.
آية رقم 91

Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.
آية رقم 96

Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,
آية رقم 97

"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."
آية رقم 98

"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.
آية رقم 99

"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."
آية رقم 108

"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
آية رقم 110

"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
آية رقم 111

Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"
آية رقم 116

Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"
آية رقم 117

Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."
آية رقم 118

"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."
آية رقم 119

Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.
آية رقم 122

Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.
آية رقم 125

"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."
آية رقم 126

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
آية رقم 128

"Shin, kunã yin ginin sitadiyo a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"
آية رقم 129

"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?"
آية رقم 130

"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."
آية رقم 131

"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
آية رقم 133

"Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya."
آية رقم 134

"Da gõnaki da marẽmari."
آية رقم 138

"Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."
آية رقم 140

Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
آية رقم 143

"Lalle ne nĩ zuwã gare ku, Manzo ne, amintacce."
آية رقم 144

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã.
آية رقم 146

"Shin, anã barin ku a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?"
آية رقم 148

"Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi mãsu narkẽwa a ciki?"
آية رقم 149

"Kuma kunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, kunã mãsu alfãhari?"
آية رقم 150

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
آية رقم 157

Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.
آية رقم 159

Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai.
آية رقم 162

"Lalle ne nĩ, zuwa gare ku, Manzõ ne, amintacce."
آية رقم 163

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
آية رقم 167

Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."
آية رقم 168

Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙĩƙa, inã daga mãsu ƙinsa."
آية رقم 169

"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."
آية رقم 170

Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.
آية رقم 173

Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya mũnana.
آية رقم 175

Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
آية رقم 178

"Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce."
آية رقم 179

"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã."
آية رقم 182

"Kuma ku yi awo da sikẽli daidaitacce."
آية رقم 184

"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko."
آية رقم 191

Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
آية رقم 192

Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.
آية رقم 196

Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.
آية رقم 200

Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
آية رقم 202

Sai ta taho musu kwatsam, alhãli kuwa sũ, ba su sansance ba.
آية رقم 203

Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne?"
آية رقم 204

Ashe, to, da azãbarMu suke nẽman gaggãwa?
آية رقم 205

Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru,
آية رقم 206

Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,
آية رقم 207

Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare su.
آية رقم 209

Dõmin tunãtarwa, kuma ba Mu kasance Mãsu zãlunci ba.
آية رقم 210

Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.
آية رقم 211

Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.
آية رقم 212

Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.
آية رقم 213

Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.
آية رقم 214

Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci.
آية رقم 216

Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."
آية رقم 218

Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye.
آية رقم 219

Da jujjuyãwarka a cikin mãsu yin sujada.
آية رقم 223

Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.
آية رقم 224

Kuma mawãƙa halakakku ne ke bin su.
آية رقم 225

Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba?
تقدم القراءة