ترجمة معاني سورة النازعات باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

آية رقم 1

An-Nazi'at


Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
آية رقم 2

Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
آية رقم 3

Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
آية رقم 4

Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
آية رقم 5

Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
آية رقم 6

Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
آية رقم 7

Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
آية رقم 8

Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
آية رقم 9

Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
آية رقم 10

Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
آية رقم 16

A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
آية رقم 19

"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
آية رقم 20

Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.
آية رقم 21

Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
آية رقم 22

Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
آية رقم 23

Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
آية رقم 25

Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
آية رقم 26

Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
آية رقم 28

Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
آية رقم 29

Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
آية رقم 33

Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
آية رقم 38

Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
آية رقم 44

Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
تقدم القراءة