ترجمة معاني سورة النازعات باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﮢﮣ
ﮤ
An-Nazi'at
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
آية رقم 2
ﮥﮦ
ﮧ
Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
آية رقم 3
ﮨﮩ
ﮪ
Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
آية رقم 4
ﮫﮬ
ﮭ
Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
آية رقم 5
ﮮﮯ
ﮰ
Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
آية رقم 6
ﮱﯓﯔ
ﯕ
Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
آية رقم 7
ﯖﯗ
ﯘ
Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
آية رقم 8
ﯙﯚﯛ
ﯜ
Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
آية رقم 9
ﯝﯞ
ﯟ
Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
آية رقم 10
ﯠﯡﯢﯣﯤ
ﯥ
Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
آية رقم 11
ﯦﯧﯨﯩ
ﯪ
"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"
آية رقم 12
ﯫﯬﯭﯮﯯ
ﯰ
Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"
آية رقم 13
ﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.
آية رقم 14
ﯶﯷﯸ
ﯹ
Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.
آية رقم 15
ﯺﯻﯼﯽ
ﯾ
Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?
آية رقم 16
ﯿﰀﰁﰂﰃﰄ
ﰅ
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
آية رقم 17
ﭑﭒﭓﭔﭕ
ﭖ
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
آية رقم 18
ﭗﭘﭙﭚﭛﭜ
ﭝ
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
آية رقم 19
ﭞﭟﭠﭡ
ﭢ
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
آية رقم 20
ﭣﭤﭥ
ﭦ
Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.
آية رقم 21
ﭧﭨ
ﭩ
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
آية رقم 22
ﭪﭫﭬ
ﭭ
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
آية رقم 23
ﭮﭯ
ﭰ
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
آية رقم 24
ﭱﭲﭳﭴ
ﭵ
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
آية رقم 25
ﭶﭷﭸﭹﭺ
ﭻ
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
آية رقم 26
ﭼﭽﭾﭿﮀﮁ
ﮂ
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
آية رقم 27
Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
آية رقم 28
ﮋﮌﮍ
ﮎ
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
آية رقم 29
ﮏﮐﮑﮒ
ﮓ
Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
آية رقم 30
ﮔﮕﮖﮗ
ﮘ
Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
آية رقم 31
ﮙﮚﮛﮜ
ﮝ
Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
آية رقم 32
ﮞﮟ
ﮠ
Da duwatsu, Yã kafe ta.
آية رقم 33
ﮡﮢﮣ
ﮤ
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
آية رقم 34
ﮥﮦﮧﮨ
ﮩ
To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
آية رقم 35
ﮪﮫﮬﮭﮮ
ﮯ
Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
آية رقم 36
ﮰﮱﯓﯔ
ﯕ
Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
آية رقم 37
ﯖﯗﯘ
ﯙ
To, amma wanda ya yi girman kai.
آية رقم 38
ﯚﯛﯜ
ﯝ
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
آية رقم 39
ﯞﯟﯠﯡ
ﯢ
To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
آية رقم 40
Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
آية رقم 41
ﯭﯮﯯﯰ
ﯱ
To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
آية رقم 42
ﯲﯳﯴﯵﯶ
ﯷ
Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?
آية رقم 43
ﯸﯹﯺﯻ
ﯼ
Me ya haɗã ka da ambatonta?
آية رقم 44
ﯽﯾﯿ
ﰀ
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
آية رقم 45
ﰁﰂﰃﰄﰅ
ﰆ
Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
آية رقم 46
Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.
تقدم القراءة