ترجمة معاني سورة القمر باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﮬﮭﮮﮯ
ﮰ
Al-Kamar
Sã'a ta yi kusa, kuma wata ya tsãge.
آية رقم 2
Kuma idan sun ga wata ãyã, sai su juya baya su ce: "Sihiri ne mai dõgẽwa!"
آية رقم 3
Kuma suka ƙaryata, kuma suka bi son zũciyarsu, alhãli kuwa kõwane al'amari (wanda suke son su tũre daga Annabi) an tabbatar da shi.
آية رقم 4
Kuma lalle, abin da yake akwai tsãwatarwa a cikinsa na lãbãraiya zo musu.
آية رقم 5
ﯪﯫﯬﯭﯮﯯ
ﯰ
Hikima cikakka! Sai dai abũbuwan gargaɗi bã su amfãni.
آية رقم 6
Sabõda haka, ka bar su! Rãnar da mai kiran zai yi kira zuwa ga wani abu abin ƙyama.
آية رقم 7
¡asƙantattu ga idanunsu zã su fito daga kaburburansu, kamar dai sũ fãri ne waɗandasuka wãtse.
آية رقم 8
Sunã gaggãwar tafiya zuwa ga mai kiran, kãfirai na cẽwa, "Wannan yini ne mai wuya!"
آية رقم 9
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata, a gabãninsu, sai suka ƙaryata BawanMu, kuma suka ce: "Shi mahaukaci ne." Kuma aka tsãwace shi.
آية رقم 10
ﭯﭰﭱﭲﭳ
ﭴ
Sabõda haka, ya kira Ubangijinsa (ya ce), "Lalle nĩ, an rinjãye ni, sai Ka yi taimako."
آية رقم 11
ﭵﭶﭷﭸﭹ
ﭺ
Sai Muka bũɗe kõfõfin sama da ruwa mai zuba.
آية رقم 12
Kuma Muka ɓuɓɓugar da ƙasã ta zama idãnun ruwa, daɗa ruwa ya haɗu a kan wani umurni da aka riga aka ƙaddara shi.
آية رقم 13
ﮅﮆﮇﮈﮉ
ﮊ
Kuma Muka ɗauke Nũhu a kan (jirgi) na alluna da ƙũsõshi.
آية رقم 14
ﮋﮌﮍﮎﮏﮐ
ﮑ
Tanã gudãna, a kan idãnunMu, dõmin sakamako ga wanda aka yi wa kãfircin.
آية رقم 15
ﮒﮓﮔﮕﮖﮗ
ﮘ
Kuma lalle, Mun bar ta ta zama ãyã. To, Shin, akwai mai tunãni
آية رقم 16
ﮙﮚﮛﮜ
ﮝ
To, yãyã azãbãTa take da gargaɗiNa?
آية رقم 17
Kuma lalle ne, haƙĩkƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ãni, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
آية رقم 18
ﮦﮧﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
Ãdãwa sun ƙaryata, to, yãya azãbãTa take, da gargaɗiNa?
آية رقم 19
Lalle Mũ, Mun aika da iska mai tsananin sauti a kansu, a cikin wani yinin nahĩsa mai dõgẽwa.
آية رقم 20
ﯘﯙﯚﯛﯜﯝ
ﯞ
Tanã fizgar mutãne kamar dai sũ kututturan dabĩno tumɓukakku ne.
آية رقم 21
ﯟﯠﯡﯢ
ﯣ
To, yãya azãbãTa take da gargaɗiNa?
آية رقم 22
Kuma lalle ne, haƙiƙa Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
آية رقم 23
ﯬﯭﯮ
ﯯ
Samũdãwa sun ƙaryata game da gargaɗin.
آية رقم 24
Sai suka ce: "Wani mutum daga cikinmu, shi kaɗai, wai mu bĩ shi! Lalle mũ a lõkacin, haƙĩƙa mun shiga wata ɓata da haukã.
آية رقم 25
"Shin, an jẽfa masa Manzancin ne, a tsakãninmu? Ã'a, shĩ dai gawurtaccen maƙaryaci ne mai girman kai!"
آية رقم 26
ﰅﰆﰇﰈﰉ
ﰊ
Zã su sani a gõbe, wãne ne gawurtaccen mai ƙaryar, mai girman kan?
آية رقم 27
Lalle Mũ, mãsu aikãwa da rãƙumar ne, ta zame musu fitina, sai ka tsare su da kallo, kuma ka yi haƙuri.
آية رقم 28
Kuma ka bã su lãbãri cẽwa ruwa rababbe ne a tsakãninsu (da rãƙumar), kõwane sha, mai shi yanã halartar sa.
آية رقم 29
ﭛﭜﭝﭞ
ﭟ
Sai suka kira abokinsu, sai ya karɓa, sa'an nan ya sõke ta,
آية رقم 30
ﭠﭡﭢﭣ
ﭤ
To, yãya azãbaTa take da gargaɗiNa?
آية رقم 31
Lalle Mũ, Mun aika tsãwa guda a kansu, sai suka kasance kamar yãyin mai shinge.
آية رقم 32
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
آية رقم 33
ﭶﭷﭸﭹ
ﭺ
Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata, game da gargaɗi.
آية رقم 34
Lalle Mun aika iskar tsakuwa a kansu, fãce mabiyan Lũɗu, Mun tsirar da su a lõkacin asuba.
آية رقم 35
Sabõda wata ni'ima ta daga gare Mu. Kamar haka Muke sãka wa wanda ya gõde.
آية رقم 36
ﮏﮐﮑﮒﮓ
ﮔ
Kuma lalle, haƙĩƙa, ya yi musu gargaɗin damƙarMu, sai suka yi musu game da gargaɗin.
آية رقم 37
Kuma lalle haƙĩƙa, su, sun nẽme shi ta wajen bãƙinsa, sai Muka shãfe idãnunsu. "To, ku ɗanɗani azãbaTa da gargaɗĩNa."
آية رقم 38
ﮟﮠﮡﮢﮣ
ﮤ
Kuma lalle, haƙĩƙa, wata azãba matabbaciya tã wãye musu gari da yãƙi, tun da sãfe.
آية رقم 39
ﮥﮦﮧ
ﮨ
To, ku ɗanɗani azãbãTa da gargaɗĩNa.
آية رقم 40
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur, ani dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
آية رقم 41
ﮱﯓﯔﯕﯖ
ﯗ
Kuma lalle, haƙĩƙa, gargaɗin ya jẽ wa mabiyan Fir'auna.
آية رقم 42
Sun ƙaryata game da ãyõyinMu, dukansu sai Muka kãma su, irin kãmun Mabuwãyi, Mai ĩkon yi.
آية رقم 43
Shin, kãfiranku ne mafi alhẽri daga waɗancan, ko kuwa kunã da wata barã'a a cikin littattafai?
آية رقم 44
ﯫﯬﯭﯮﯯ
ﯰ
Kõ zã su ce: "Mũ duka mãsu haɗa ƙarfi ne dõmin cin nasara?"
آية رقم 45
ﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Zã a karya tãron, kuma su jũya bãya dõmin gudu.
آية رقم 46
ﯶﯷﯸﯹﯺﯻ
ﯼ
Ã'a, Sã'a ita cẽ lõkacin wa'adinsu, kuma Sã'ar tã fi tsananin masĩfa, kuma ta fiɗãci.
آية رقم 47
ﯽﯾﯿﰀﰁ
ﰂ
Lalle ne, mãsu laifi sunã a cikin ɓata da hauka.
آية رقم 48
Rãnar da zã a jã su a cikin wuta a kan fuskõkinsu. "Ku ɗanɗani shãfar wutar Saƙar."
آية رقم 49
ﰍﰎﰏﰐﰑ
ﰒ
Lalle Mũ, kõwane irin abu Mun halitta shi a kan tsãri.
آية رقم 50
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
Kuma umurninMu bai zamo ba fãce da kalma ɗaya, kamar walƙãwar ido.
آية رقم 51
ﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
ﭞ
Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun halaka irin gayyarku. To, shin, akwai mai tunãni?
آية رقم 52
ﭟﭠﭡﭢﭣ
ﭤ
Kuma kõwane abu, da suka aikata shi, yanã a cikin littattafai.
آية رقم 53
ﭥﭦﭧﭨ
ﭩ
Kuma dukkan ƙarami da babba, rubutacce ne.
آية رقم 54
ﭪﭫﭬﭭﭮ
ﭯ
Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna da kõguna.
آية رقم 55
ﭰﭱﭲﭳﭴﭵ
ﭶ
A cikin mazaunin gaskiya, wurin Mai ikon yi, Mai iya zartaswa.
تقدم القراءة