ترجمة معاني سورة الشعراء باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﭑ
ﭒ
As-Shu'ara
¦. S̃. M̃.
آية رقم 2
ﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.
آية رقم 3
ﭘﭙﭚﭛﭜﭝ
ﭞ
Tsammãninka kai mai halakar da ranka ne, dõmin ba su kasance mũminai ba!
آية رقم 4
Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai.
آية رقم 5
Kuma wata tunãtarwa ba ta jẽ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirẽwa.
آية رقم 6
To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.
آية رقم 7
Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau?
آية رقم 8
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba.
آية رقم 9
ﮖﮗﮘﮙﮚ
ﮛ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.
آية رقم 10
Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai.
آية رقم 11
ﮥﮦﮧﮨﮩ
ﮪ
"Mutãnen Fir'auna bã zã su yi taƙawa ba?"
آية رقم 12
ﮫﮬﮭﮮﮯﮰ
ﮱ
Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni.
آية رقم 13
"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.
آية رقم 14
ﯜﯝﯞﯟﯠﯡ
ﯢ
"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."
آية رقم 15
Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre."
آية رقم 16
"Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne."
آية رقم 17
ﯵﯶﯷﯸﯹ
ﯺ
"Ka saki Banĩ Isrã'ila tãre da mu."
آية رقم 18
Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?"
آية رقم 19
"Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?"
آية رقم 20
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin hushi."
آية رقم 21
"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."
آية رقم 22
"Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla."
آية رقم 23
ﭭﭮﭯﭰﭱ
ﭲ
Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"
آية رقم 24
Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."
آية رقم 25
ﭾﭿﮀﮁﮂ
ﮃ
Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?"
آية رقم 26
ﮄﮅﮆﮇﮈ
ﮉ
Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko."
آية رقم 27
Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne."
آية رقم 28
Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta."
آية رقم 29
Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."
آية رقم 30
ﮦﮧﮨﮩﮪ
ﮫ
Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"
آية رقم 31
Ya ce: "To, ka zõ da shi idan ka kasance daga, mãsu gaskiya."
آية رقم 32
ﯕﯖﯗﯘﯙﯚ
ﯛ
Sai ya jẽfa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne.
آية رقم 33
ﯜﯝﯞﯟﯠﯡ
ﯢ
Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu kallo.
آية رقم 34
(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!
آية رقم 35
"Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mẽne ne kuke shãwartãwa?"
آية رقم 36
Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."
آية رقم 37
ﯼﯽﯾﯿ
ﰀ
"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."
آية رقم 38
ﰁﰂﰃﰄﰅ
ﰆ
Sai aka tãra masihirta dõmin ajalin yini sananne.
آية رقم 39
ﰇﰈﰉﰊﰋ
ﰌ
Kuma aka ce wa mutãne "Kõ kũ mãsu tãruwã ne?
آية رقم 40
"Tsammãninmu mu bi masihirta, idan sun kasance sũ ne marinjãya."
آية رقم 41
To, a lõkacin da masihirta suka jẽ suka ce wa Fir'auna,"Shin, lalle ne, haƙĩƙa munã da ijãra idan mun kasance mũ ne marinjãya?"
آية رقم 42
ﭦﭧﭨﭩﭪﭫ
ﭬ
Ya ce: "Na'am! Kuma lalle ne, kũ ne a lõkacin haƙĩƙa muƙarrabai."
آية رقم 43
Mũsã ya ce musu, "Ku jẽfa abin da kuke mãsu jẽfãwa."
آية رقم 44
Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."
آية رقم 45
Sai Mũsa ya jẽfa sandarsa, sai ga ta tanã harhaɗe abin da suke yi na ƙarya.
آية رقم 46
ﮈﮉﮊ
ﮋ
Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.
آية رقم 47
ﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta."
آية رقم 48
ﮑﮒﮓ
ﮔ
"Ubangijin Mũsa da Hãrũna."
آية رقم 49
Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa, zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrẽ ku gabã ɗaya."
آية رقم 50
Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."
آية رقم 51
"Lalle ne mu munã kwaɗayin Ubangijinmu, Ya gãfarta mana kurakuranmu dõmin mun kasance farkon mãsu ĩmãni."
آية رقم 52
Kuma Muka aika zuwa ga Mũsã cẽwa ka yi tafiyar dare da bãyiNa, lalle ne kũ waɗanda ake biyã ne.
آية رقم 53
ﯭﯮﯯﯰﯱ
ﯲ
Sai Fir'auna ya aika mãsu gayya a cikin birãne.
آية رقم 54
ﯳﯴﯵﯶ
ﯷ
"Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan."
آية رقم 55
ﯸﯹﯺ
ﯻ
"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."
آية رقم 56
ﯼﯽﯾ
ﯿ
"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."
آية رقم 57
ﰀﰁﰂﰃ
ﰄ
Sai Muka fitar da su daga gonaki da marẽmari.
آية رقم 58
ﰅﰆﰇ
ﰈ
Da taskõki da mazauni mai kyau.
آية رقم 59
ﰉﰊﰋﰌﰍ
ﰎ
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da su ga Banĩ Isrãĩla.
آية رقم 60
ﰏﰐ
ﰑ
Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.
آية رقم 61
Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."
آية رقم 62
Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni."
آية رقم 63
Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cẽwa "Ka dõki tẽku da sandarka." Sai tẽku ta tsãge, kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma.
آية رقم 64
ﭱﭲﭳ
ﭴ
Kuma Muka kusantar da waɗansu mutãne a can.
آية رقم 65
ﭵﭶﭷﭸﭹ
ﭺ
Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.
آية رقم 66
ﭻﭼﭽ
ﭾ
Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.
آية رقم 67
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
آية رقم 68
ﮉﮊﮋﮌﮍ
ﮎ
Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.
آية رقم 69
ﮏﮐﮑﮒ
ﮓ
Kuma ka karanta, a kansu, lãbãrin Ibrãhĩm.
آية رقم 70
ﮔﮕﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
A sã'ilin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bauta wa?"
آية رقم 71
ﮛﮜﮝﮞﮟﮠ
ﮡ
Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."
آية رقم 72
ﮢﮣﮤﮥﮦ
ﮧ
Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira?"
آية رقم 73
ﮨﮩﮪﮫ
ﮬ
"Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?"
آية رقم 74
ﮭﮮﮯﮰﮱﯓ
ﯔ
Suka ce: "Ã'a mun sãmĩ ubanninmu, kamar haka ne suke aikatãwa."
آية رقم 75
ﯕﯖﯗﯘﯙ
ﯚ
Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?"
آية رقم 76
ﯛﯜﯝ
ﯞ
"Kũ da ubanninku mafi daɗẽwa?"
آية رقم 77
ﯟﯠﯡﯢﯣﯤ
ﯥ
"To lalle ne, sũ maƙiya ne a gare ni, fãce Ubangijin halittu."
آية رقم 78
ﯦﯧﯨﯩ
ﯪ
"Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni."
آية رقم 79
ﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."
آية رقم 80
ﯰﯱﯲﯳ
ﯴ
"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."
آية رقم 81
ﯵﯶﯷﯸ
ﯹ
"Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni."
آية رقم 82
"Kuma wanda Yake inã kwaɗayin Ya gãfarta mini kurãkuraina, a rãnar sãkamako."
آية رقم 83
ﰃﰄﰅﰆﰇﰈ
ﰉ
"Ya Ubangijĩna! Ka ba ni hukunci, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai."
آية رقم 84
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya a cikin mutãnen ƙarshe."
آية رقم 85
ﭘﭙﭚﭛﭜ
ﭝ
"Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni'ima."
آية رقم 86
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣ
ﭤ
"Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu."
آية رقم 87
ﭥﭦﭧﭨ
ﭩ
"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."
آية رقم 88
ﭪﭫﭬﭭﭮﭯ
ﭰ
"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."
آية رقم 89
ﭱﭲﭳﭴﭵﭶ
ﭷ
"Fãce wanda ya jẽ wa Allah da zũciya mai tsarki."
آية رقم 90
ﭸﭹﭺ
ﭻ
Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.
آية رقم 91
ﭼﭽﭾ
ﭿ
Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.
آية رقم 92
ﮀﮁﮂﮃﮄﮅ
ﮆ
Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?"
آية رقم 93
"Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?"
آية رقم 94
ﮏﮐﮑﮒ
ﮓ
Sai aka kikkife su a cikinta, su da halakakkun.
آية رقم 95
ﮔﮕﮖ
ﮗ
Da rundunar Ibilĩsa gabã ɗaya.
آية رقم 96
ﮘﮙﮚﮛ
ﮜ
Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,
آية رقم 97
ﮝﮞﮟﮠﮡﮢ
ﮣ
"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."
آية رقم 98
ﮤﮥﮦﮧ
ﮨ
"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.
آية رقم 99
ﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."
آية رقم 100
ﮮﮯﮰﮱ
ﯓ
"Sabõda haka bã mu da waɗansu macẽta."
آية رقم 101
ﯔﯕﯖ
ﯗ
"Kuma bã mu da abõki, masõyi."
آية رقم 102
"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"
آية رقم 103
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba.
آية رقم 104
ﯪﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
آية رقم 105
ﯰﯱﯲﯳ
ﯴ
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni.
آية رقم 106
A lõkacin da ɗan'uwansu, Nũhu, ya ce musu, "Shin, bã zã ku yi taƙawa ba?"
آية رقم 107
ﯽﯾﯿﰀ
ﰁ
"Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce."
آية رقم 108
ﰂﰃﰄ
ﰅ
"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
آية رقم 109
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãtã ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
آية رقم 110
ﰓﰔﰕ
ﰖ
"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
آية رقم 111
ﰗﰘﰙﰚﰛﰜ
ﰝ
Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"
آية رقم 112
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa."
آية رقم 113
"Hisãbinsu bai zama ba fãce ga Ubangijina, dã kunã sansancẽwa."
آية رقم 114
ﭡﭢﭣﭤ
ﭥ
"Ban zama mai kõre mũminai ba."
آية رقم 115
ﭦﭧﭨﭩﭪ
ﭫ
"Nĩ ba kõwa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanãwa."
آية رقم 116
Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"
آية رقم 117
ﭵﭶﭷﭸﭹ
ﭺ
Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."
آية رقم 118
"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."
آية رقم 119
ﮅﮆﮇﮈﮉﮊ
ﮋ
Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.
آية رقم 120
ﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
Sa'an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran.
آية رقم 121
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
آية رقم 122
ﮛﮜﮝﮞﮟ
ﮠ
Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.
آية رقم 123
ﮡﮢﮣ
ﮤ
Ãdãwa sun ƙaryata Manzanni.
آية رقم 124
A lõkacin da ɗan'uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
آية رقم 125
ﮭﮮﮯﮰ
ﮱ
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."
آية رقم 126
ﯓﯔﯕ
ﯖ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
آية رقم 127
"Kuma bã ni tambayar wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba, fãce daga Ubangijin halittu."
آية رقم 128
ﯤﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
"Shin, kunã yin ginin sitadiyo a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"
آية رقم 129
ﯪﯫﯬﯭ
ﯮ
"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?"
آية رقم 130
ﯯﯰﯱﯲ
ﯳ
"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."
آية رقم 131
ﯴﯵﯶ
ﯷ
"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
آية رقم 132
ﯸﯹﯺﯻﯼ
ﯽ
"Ku ji tsõron wanda Ya taimake ku da abin da kuka sani."
آية رقم 133
ﯾﯿﰀ
ﰁ
"Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya."
آية رقم 134
ﰂﰃ
ﰄ
"Da gõnaki da marẽmari."
آية رقم 135
ﰅﰆﰇﰈﰉﰊ
ﰋ
"Lalle ne nĩ, inã ji muku tsõron azãbar wani yini mai girma."
آية رقم 136
Suka ce: "Daidai ne a kanmu: Kã yi wa'azi kõ ba ka kasance daga mãsu wa'azi ba."
آية رقم 137
ﭑﭒﭓﭔﭕ
ﭖ
"Wannan abu bai zamõ ba fãce hãlãyen mutãnen farko."
آية رقم 138
ﭗﭘﭙ
ﭚ
"Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."
آية رقم 139
Sabõda haka suka ƙaryata shi, sai Muka halakar da sũ. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
آية رقم 140
ﭨﭩﭪﭫﭬ
ﭭ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
آية رقم 141
ﭮﭯﭰ
ﭱ
Samũdãwa sun ƙaryata Manzanni.
آية رقم 142
A lõkacin da ɗan'uwansu Sãlihu ya ce: "Shin, bã zã ku bi Allah da taƙawa ba?"
آية رقم 143
ﭺﭻﭼﭽ
ﭾ
"Lalle ne nĩ zuwã gare ku, Manzo ne, amintacce."
آية رقم 144
ﭿﮀﮁ
ﮂ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã.
آية رقم 145
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba fãce da a Ubangijin halittu."
آية رقم 146
ﮐﮑﮒﮓﮔ
ﮕ
"Shin, anã barin ku a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?"
آية رقم 147
ﮖﮗﮘ
ﮙ
"A cikin gõnaki da marẽmari."
آية رقم 148
ﮚﮛﮜﮝ
ﮞ
"Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi mãsu narkẽwa a ciki?"
آية رقم 149
ﮟﮠﮡﮢﮣ
ﮤ
"Kuma kunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, kunã mãsu alfãhari?"
آية رقم 150
ﮥﮦﮧ
ﮨ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
آية رقم 151
ﮩﮪﮫﮬ
ﮭ
"Kada ku yi ɗã'ã ga umurnin maɓarnata."
آية رقم 152
ﮮﮯﮰﮱﯓﯔ
ﯕ
"Waɗanda suke yin ɓarna a cikin ƙasa, kuma bã su kyautatãwa."
آية رقم 153
ﯖﯗﯘﯙﯚ
ﯛ
Suka ce: "Kai daga mãsu sihiri kurum kake."
آية رقم 154
"Bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu. To, kã zo da wata ãyã idan kã kasance daga mãsu gaskiya."
آية رقم 155
Ya ce: "Wannan rãkuma ce tanã da shan yini, kuma kunã da shan yini sasanne."
آية رقم 156
"Kada ku shãfe ta da cũta har azãbar yini mai girmã ta shãfe ku."
آية رقم 157
ﯺﯻﯼ
ﯽ
Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.
آية رقم 158
Sabõda haka azãba ta kãma su. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
آية رقم 159
ﰋﰌﰍﰎﰏ
ﰐ
Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai.
آية رقم 160
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata Manzanni.
آية رقم 161
A lõkacin da ɗan'uwansu, Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
آية رقم 162
ﭞﭟﭠﭡ
ﭢ
"Lalle ne nĩ, zuwa gare ku, Manzõ ne, amintacce."
آية رقم 163
ﭣﭤﭥ
ﭦ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
آية رقم 164
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra, Ijãrãta ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
آية رقم 165
ﭴﭵﭶﭷ
ﭸ
"Shin kunã jẽ wa maza daga cikin talikai?"
آية رقم 166
"Kuma kunã barin abin da Ubangijinku Ya halitta muku daga mãtanku? Ã'a, ku mutãne ne mãsu ƙẽtarẽwa!"
آية رقم 167
Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."
آية رقم 168
ﮏﮐﮑﮒﮓ
ﮔ
Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙĩƙa, inã daga mãsu ƙinsa."
آية رقم 169
ﮕﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."
آية رقم 170
ﮛﮜﮝ
ﮞ
Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.
آية رقم 171
ﮟﮠﮡﮢ
ﮣ
Fãce wata tsõhuwa a cikin mãsu wanzuwa.
آية رقم 172
ﮤﮥﮦ
ﮧ
Sa'an nan kuma Muka darkãke wasu.
آية رقم 173
Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya mũnana.
آية رقم 174
Lalle ne ga wannan, akwai ãyã, kuma mafi yawansu bã su kasance mãsu ĩmãni ba.
آية رقم 175
ﯛﯜﯝﯞﯟ
ﯠ
Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
آية رقم 176
ﯡﯢﯣﯤ
ﯥ
Ma'abũta ƙunci sun ƙaryata Manzanni.
آية رقم 177
ﯦﯧﯨﯩﯪﯫ
ﯬ
A lõkacin da Shu'aibu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
آية رقم 178
ﯭﯮﯯﯰ
ﯱ
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce."
آية رقم 179
ﯲﯳﯴ
ﯵ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã."
آية رقم 180
"Kuma ba ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
آية رقم 181
"Ku cika mũdu, kuma kada ku kasance daga mãsu sanyãwar hasãra (ga mutãne)."
آية رقم 182
ﰋﰌﰍ
ﰎ
"Kuma ku yi awo da sikẽli daidaitacce."
آية رقم 183
"Kuma kada ku nakasa wa mutãne abũbuwansu kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa kuna mãsu ɓarna."
آية رقم 184
ﭑﭒﭓﭔﭕ
ﭖ
"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko."
آية رقم 185
ﭗﭘﭙﭚﭛ
ﭜ
Suka ce: "Kai dai daga waɗanda suke sihirtattu kawai ne."
آية رقم 186
"Kuma bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu kuma lalle ne munã zaton ka, haƙĩƙa, daga maƙaryata."
آية رقم 187
"To ka jẽfo wani ɓaɓɓake daga sama a kanmu, idan ka kasance daga mãsu gaskiya."
آية رقم 188
ﭱﭲﭳﭴﭵ
ﭶ
Ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga abin da kuke aikatãwa."
آية رقم 189
Sai suka ƙaiyatã shi, sabõda haka, azãbar rãnar girgije ta kãma su. Lalle ne ita, tã kasance azãbar yini mai girma.
آية رقم 190
Lalle a cikin wancan haƙĩka akwai ãya, amma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
آية رقم 191
ﮍﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
آية رقم 192
ﮓﮔﮕﮖ
ﮗ
Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.
آية رقم 193
ﮘﮙﮚﮛ
ﮜ
Rũhi amintacce ne ya sauka da shi.
آية رقم 194
ﮝﮞﮟﮠﮡ
ﮢ
A kan zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.
آية رقم 195
ﮣﮤﮥ
ﮦ
Da harshe na Larabci mai bayãni.
آية رقم 196
ﮧﮨﮩﮪ
ﮫ
Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.
آية رقم 197
Ashe, bai kasance ãyã ba a gare su, ya zama Mãlaman Banĩ Isrã'ĩla sun san shi?
آية رقم 198
ﯗﯘﯙﯚﯛ
ﯜ
Kuma dã mun saukar da shi a kan sãshen Ajamãwa,
آية رقم 199
ﯝﯞﯟﯠﯡﯢ
ﯣ
Ya karanta shi a kansu, ba su kasance sabõda shi mãsu ĩmãni ba.
آية رقم 200
ﯤﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
آية رقم 201
Bã zã su yi ĩmãni da shĩ ba sai sun ga azãbar nan mai raɗadi.
آية رقم 202
ﯲﯳﯴﯵﯶ
ﯷ
Sai ta taho musu kwatsam, alhãli kuwa sũ, ba su sansance ba.
آية رقم 203
ﯸﯹﯺﯻ
ﯼ
Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne?"
آية رقم 204
ﯽﯾ
ﯿ
Ashe, to, da azãbarMu suke nẽman gaggãwa?
آية رقم 205
ﰀﰁﰂﰃ
ﰄ
Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru,
آية رقم 206
ﰅﰆﰇﰈﰉ
ﰊ
Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,
آية رقم 207
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare su.
آية رقم 208
Kuma bã Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da mãsu gargaɗi.
آية رقم 209
ﭠﭡﭢﭣ
ﭤ
Dõmin tunãtarwa, kuma ba Mu kasance Mãsu zãlunci ba.
آية رقم 210
ﭥﭦﭧﭨ
ﭩ
Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.
آية رقم 211
ﭪﭫﭬﭭﭮ
ﭯ
Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.
آية رقم 212
ﭰﭱﭲﭳ
ﭴ
Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.
آية رقم 213
Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.
آية رقم 214
ﭿﮀﮁ
ﮂ
Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci.
آية رقم 215
ﮃﮄﮅﮆﮇﮈ
ﮉ
Kuma ka sassauta fikãfikanka ga wanda ya bĩ ka daga mũminai.
آية رقم 216
Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."
آية رقم 217
ﮒﮓﮔﮕ
ﮖ
Kuma ka dõgara ga Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
آية رقم 218
ﮗﮘﮙﮚ
ﮛ
Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye.
آية رقم 219
ﮜﮝﮞ
ﮟ
Da jujjuyãwarka a cikin mãsu yin sujada.
آية رقم 220
ﮠﮡﮢﮣ
ﮤ
Lalle Shi, Shi ne Mai ji, Masani.
آية رقم 221
ﮥﮦﮧﮨﮩﮪ
ﮫ
Shin, (kunã so) in gaya muku a kan wanda Shaiɗãnnu kan sauka?
آية رقم 222
ﮬﮭﮮﮯﮰ
ﮱ
Sukan sauka a kan dukkan maƙaryaci, mai zunubi.
آية رقم 223
ﯓﯔﯕﯖ
ﯗ
Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.
آية رقم 224
ﯘﯙﯚ
ﯛ
Kuma mawãƙa halakakku ne ke bin su.
آية رقم 225
Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba?
آية رقم 226
ﯤﯥﯦﯧﯨ
ﯩ
Kuma lalle ne, sũ, sunã faɗin abin da bã su aikatãwa?
آية رقم 227
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka ambaci Allah da yawa, kuma suka rãma zãlunci, daga bãyan an zãlunce su. Kuma waɗanda suka yi zãlunci, zã su sani a wace majũya suke jũyãwa.
تقدم القراءة