ترجمة معاني سورة الحجر باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

آية رقم 6

Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur'ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne."

Bã Mu sassaukar da malã'iku fãce da gaskiya, bã zã su kasance, a wannan lõkacin, waɗanda ake yi wa jinkĩri ba.
آية رقم 9

Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lal1e Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi.
آية رقم 12

Kamar wancan ne Muke shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
آية رقم 15

Lalle ne dã sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idãnuwanmu ne. Ã'a, mũ mutãne ne waɗanda aka sihirce."
آية رقم 16

Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya waɗansu masaukai a, cikin sama, kuma Muka ƙawãta ta ga masu kallo.

Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikẽli.
آية رقم 20

Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba.

Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa'an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacẽwa a gare shi ba.
آية رقم 24

Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri.

"To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada."
آية رقم 34

Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai abin jĩfa ne."
آية رقم 36

Ya ce: "Yã Ubangjĩna! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa rãnar da ake tãshin su."
آية رقم 37

Ya ce: "To, lalle ne kanã daga waɗanda ake yi wa jinkiri."

Ya ce: "Yã Ubangijina! Inã rantsuwa da abin da Ka ɓatar da ni da shi, haƙĩƙa inã ƙawãta musu (rãyuwa) a cikin ƙasã kuma haƙĩƙa inã ɓatar da su gabã ɗaya."
آية رقم 40

"Fãce bãyinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake."
آية رقم 43

Kuma lalle Jahannama ce haƙĩƙa, ma'a1kawartarsu gabã ɗaya.
آية رقم 45

Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna mai idandunan ruwa.
آية رقم 46

"Ku shigẽ ta da aminci, kunã amintattu."

Kuma Muka ɗẽbe abinda ke a cikin zukãtansu na daga ƙullin zũci, suka zama 'yan'uwa a kan gadãje, sunã mãsu fuskantar junã.
آية رقم 53

Suka ce: "Kada ka firgita. Lalle ne mũ, munã yi makabushãra game da wani yãro masani."
آية رقم 55

Suka ce: "Munã yi maka bushãra da gaskiya ne, sabõda haka, kada da kasance daga mãsu yanke tsammãni."
آية رقم 59

"Fãce mutãnen Lũɗu, lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu tsĩrar dasu ne gabã ɗaya."
آية رقم 60

"Fãce mãtarsa mun ƙaddara cẽwa lalle ne ita, haƙĩƙa, tanã daga mãsu halaka."
آية رقم 62

Ya ce: "Lalle ne ku mutãne ne waɗanda ba a sani ba."
آية رقم 64

"Kuma mun zo maka da gaskiya. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu gaskiya ne."

Kuma Muka hukunta wancan al'amarin zuwa gare shi cẽwa lalle ne ƙarshen waɗancan abin yankẽwa ne a lõkacin da suke mãsu shiga asuba.
آية رقم 67

Kuma mutãnen alƙaryar suka je sunã mãsu bushãra.
آية رقم 68

Ya ce: "Lalle ne waɗannan bãƙĩna ne, sabõda haka kada ku kunyata ni."
آية رقم 69

"Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku sanya ni a baƙin ciki."
آية رقم 72

Rantsuwa da rãyuwarka! Lalle ne sũ a cikin mãyensu sunã ta ɗĩmuwa.
آية رقم 73

Sa'an nan tsãwa ta kãma su, sunã mãsu shiga lõkacin hũdõwar rãnã.
آية رقم 74

Sa'an nan Muka sanya samanta ya kõma ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu na lãkar wuta a kansu.
آية رقم 75

Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu tsõkaci da hankali.
آية رقم 76

Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa sunã a gẽfen wata hanyã tabbatacciya.
آية رقم 78

Kuma lalle ne ma'abũta Al'aika sun kasance, haƙĩƙa, mãsu zãlunci!
آية رقم 79

Sai Muka yi azãbar rãmuwã a gare su, kuma lalle sũ biyun, haƙĩƙa, sunã a gẽfen wani tafarki mabayyani.
آية رقم 80

Kuma lalle ne haƙĩƙa ma'abũta Hijiri sun ƙaryata Manzanni.
آية رقم 81

Kuma Kuka kai musu ãyõyinMu, sai suka kasance mãsu bijirẽwa daga gare su.
آية رقم 82

Kuma sun kasance sunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, alhãli sunã amintattu.
آية رقم 83

Sai tsãwa ta kãma su sunã mãsu shiga asuba.
آية رقم 84

Sa'an nan abin da suka kasance sunã tsirfantãwa bai wadãtar ga barinsu ba.

Kuma ba Mu halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu ba fãce da gaskiya. Kuma lalle ne Sã'a (Rãnar Alƙiyãma) haƙĩƙa mai zuwa ce. Sabõdahaka ka yi rangwame, rangwame mai kyau.
آية رقم 87

Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bã ka bakwai waɗanda ake maimaita karatunsu da Alƙur'ãni mai girma.

Kada lalle kaƙĩƙa idãnunka biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi game da shi, nau'i-nau'i a gare su, kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma sassauta fikãfikanka ga mãsu ĩmãni.
آية رقم 92

To, rantsuwa da Ubangijinka! Haƙĩƙa, Munã tambayarsugabã ɗaya.
آية رقم 93

Daga abin da suka kasance sunã aikatãwa.
آية رقم 94

Sai ka tsage gaskiya game da abin da ake umurnin ka kuma ka kau da kai daga masu shirki.
آية رقم 95

Lalle ne Mũ Mun isar maka daga mãsu izgili.
آية رقم 97

Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã sanin cẽwa lalle kai, ƙirjinka yanã yin ƙunci game da abin da suke faɗã (na izgili).
آية رقم 98

Sabõda haka ka yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka kasance daga mãsu sujada.
تقدم القراءة