ترجمة معاني سورة الحجر باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
A-Hijr
A. L̃.R. Waɗancan ãyoyin littãfi ne da abin karantãwa mai bayyanãwa.
آية رقم 2
Da yawa waɗanda suka kãfirta suke gũrin dã dai sun kasance Musulmi.
آية رقم 3
Ka bar su su ci kuma su ji dãdi, kuma gũri ya shagaltar da su, sa'an nan da sannu zã su sani.
آية رقم 4
Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da littafi sananne.
آية رقم 5
Wata al'umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba.
آية رقم 6
Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur'ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne."
آية رقم 7
"Dõmin me bã zã ka zo mana da malã'ĩku ba idan ka kasance daga mãsu gaskiya?"
آية رقم 8
Bã Mu sassaukar da malã'iku fãce da gaskiya, bã zã su kasance, a wannan lõkacin, waɗanda ake yi wa jinkĩri ba.
آية رقم 9
Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lal1e Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi.
آية رقم 10
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika Manzanni a cikin ƙungiyõyin farko, gabãninka.
آية رقم 11
Kuma wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu, izgili a gare shi.
آية رقم 12
ﮰﮱﯓﯔﯕ
ﯖ
Kamar wancan ne Muke shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
آية رقم 13
Bã su yin ĩmãni da shi, kuma haƙĩƙa, hanyar mutãnen farko ta shige.
آية رقم 14
Kuma dã Mun bũɗe wata ƙõfa daga sama a kansu har suka wuni a ciki sunã tãkãwa.
آية رقم 15
Lalle ne dã sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idãnuwanmu ne. Ã'a, mũ mutãne ne waɗanda aka sihirce."
آية رقم 16
Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya waɗansu masaukai a, cikin sama, kuma Muka ƙawãta ta ga masu kallo.
آية رقم 17
ﭙﭚﭛﭜﭝ
ﭞ
Kuma Muka kiyãye ta daga dukan Shaiɗani wanda ake jĩfa.
آية رقم 18
Fãce wanda ya sãci saurãre sai wutar yũlã bayyananniya ta bĩ shi.
آية رقم 19
Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikẽli.
آية رقم 20
Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba.
آية رقم 21
Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne.
آية رقم 22
Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa'an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacẽwa a gare shi ba.
آية رقم 23
ﮕﮖﮗﮘﮙﮚ
ﮛ
Kuma lalle ne Mu Muke rãyarwa, kuma Muke kashẽwa kuma Mũ ne magada.
آية رقم 24
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri.
آية رقم 25
Kuma lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Yake tãra su, lalle Shĩ ne Mai hikima, Masani.
آية رقم 26
Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar lãka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja.
آية رقم 27
Kuma Aljani Mun haliccẽ shi daga gabãni, daga wutar iskar zafi.
آية رقم 28
Kuma a lõkacin da Ubangijinka ya ce wa malã'iku: "Lalle Nĩ mai halittar wani jiki ne daga ƙẽƙasasshen yumɓu wanda ya canja."
آية رقم 29
"To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada."
آية رقم 30
ﯶﯷﯸﯹ
ﯺ
Sai malã'iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya.
آية رقم 31
Fãce Iblĩs, ya ƙi kasancẽwa daga mãsu yin sujadar.
آية رقم 32
Ya ce: "Yã Iblĩs mẽne ne a gare ka, ba ka kasance tãre da mãsu yin sujuda ba?"
آية رقم 33
Ya ce: "Ban kasance inã yin sujada ba ga mutum wanda Ka halicce shi daga bũsasshen yumɓun lãka wadda ta canja."
آية رقم 34
ﭦﭧﭨﭩﭪ
ﭫ
Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai abin jĩfa ne."
آية رقم 35
ﭬﭭﭮﭯﭰﭱ
ﭲ
"Kuma lalle ne akwai la'ana a kanka har ya zuwa rãnar sakamako."
آية رقم 36
ﭳﭴﭵﭶﭷﭸ
ﭹ
Ya ce: "Yã Ubangjĩna! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa rãnar da ake tãshin su."
آية رقم 37
ﭺﭻﭼﭽ
ﭾ
Ya ce: "To, lalle ne kanã daga waɗanda ake yi wa jinkiri."
آية رقم 38
ﭿﮀﮁﮂ
ﮃ
"Zuwa ga Yinin Lõkacin nan sananne."
آية رقم 39
Ya ce: "Yã Ubangijina! Inã rantsuwa da abin da Ka ɓatar da ni da shi, haƙĩƙa inã ƙawãta musu (rãyuwa) a cikin ƙasã kuma haƙĩƙa inã ɓatar da su gabã ɗaya."
آية رقم 40
ﮏﮐﮑﮒ
ﮓ
"Fãce bãyinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake."
آية رقم 41
ﮔﮕﮖﮗﮘ
ﮙ
Ya ce: "Wannan tafarki ne a gare Ni, madaidaici."
آية رقم 42
"Lalle ne bãyĩNa, bã ka da ĩkõ a kansu, fãce wanda ya bĩ ka daga ɓatattu."
آية رقم 43
ﮦﮧﮨﮩ
ﮪ
Kuma lalle Jahannama ce haƙĩƙa, ma'a1kawartarsu gabã ɗaya.
آية رقم 44
Tanã da ƙõfõfi bakwai, ga kõwace ƙõfa akwai wani juz'i daga gare su rababbe.
آية رقم 45
ﯕﯖﯗﯘﯙ
ﯚ
Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna mai idandunan ruwa.
آية رقم 46
ﯛﯜﯝ
ﯞ
"Ku shigẽ ta da aminci, kunã amintattu."
آية رقم 47
Kuma Muka ɗẽbe abinda ke a cikin zukãtansu na daga ƙullin zũci, suka zama 'yan'uwa a kan gadãje, sunã mãsu fuskantar junã.
آية رقم 48
Wata wahala bã zã ta shãfe su bã a cikinta kuma ba su zama mãsu fita daga, cikinta ba.
آية رقم 49
Ka bai wa bãyiNa lãbari cẽwa lalle ne Ni, Mai gãfarane, Mai jin ƙai.
آية رقم 50
ﯻﯼﯽﯾﯿ
ﰀ
Kuma azãbãTa ita ce azãba mai raɗaɗi.
آية رقم 51
ﰁﰂﰃﰄ
ﰅ
Kuma ka bã su lãbãrin bãƙin Ibrãhĩm.
آية رقم 52
A lõkacin da suka shiga gunsa, sai suka ce: "Sallama." Ya ce: "Lalle mũ, daga gare ku, mãsu firgita ne."
آية رقم 53
Suka ce: "Kada ka firgita. Lalle ne mũ, munã yi makabushãra game da wani yãro masani."
آية رقم 54
Ya ce: "Shin kun bã ni bushãra ne a kan tsũfa yã shãfe ni? To, da me kuke bã ni bushara?"
آية رقم 55
Suka ce: "Munã yi maka bushãra da gaskiya ne, sabõda haka, kada da kasance daga mãsu yanke tsammãni."
آية رقم 56
Ya ce: "Kuma wãne ne yake yanke tsammãni daga rahamar Ubangijinsa, fãce ɓatattu?"
آية رقم 57
ﭽﭾﭿﮀﮁ
ﮂ
Ya ce: "To, mẽne ne babban al'amarinku? Yã kũ manzanni!"
آية رقم 58
ﮃﮄﮅﮆﮇﮈ
ﮉ
Suka ce: "Lalle ne mũ, an aika mu zuwa ga wasu mutãne mãsu laifi."
آية رقم 59
ﮊﮋﮌﮍﮎﮏ
ﮐ
"Fãce mutãnen Lũɗu, lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu tsĩrar dasu ne gabã ɗaya."
آية رقم 60
ﮑﮒﮓﮔﮕﮖ
ﮗ
"Fãce mãtarsa mun ƙaddara cẽwa lalle ne ita, haƙĩƙa, tanã daga mãsu halaka."
آية رقم 61
ﮘﮙﮚﮛﮜ
ﮝ
To, a lõkacin da mazannin suka jẽ wa mutãnen Lũɗu,
آية رقم 62
ﮞﮟﮠﮡ
ﮢ
Ya ce: "Lalle ne ku mutãne ne waɗanda ba a sani ba."
آية رقم 63
Suka ce: "Ã'a, mun zo maka sabõda abin da suka kasance sunã shakka a cikinsa."
آية رقم 64
ﮫﮬﮭﮮ
ﮯ
"Kuma mun zo maka da gaskiya. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu gaskiya ne."
آية رقم 65
"Sai ka yi tafiya da iyãlinka, a wani yanki na dare, kuma ka bi bãyansu, kuma kada wani daga cikinku ya yi waiwaye, kuma ku bi ta inda aka aumurce ku."
آية رقم 66
Kuma Muka hukunta wancan al'amarin zuwa gare shi cẽwa lalle ne ƙarshen waɗancan abin yankẽwa ne a lõkacin da suke mãsu shiga asuba.
آية رقم 67
ﯪﯫﯬﯭ
ﯮ
Kuma mutãnen alƙaryar suka je sunã mãsu bushãra.
آية رقم 68
ﯯﯰﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Ya ce: "Lalle ne waɗannan bãƙĩna ne, sabõda haka kada ku kunyata ni."
آية رقم 69
ﯶﯷﯸﯹ
ﯺ
"Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku sanya ni a baƙin ciki."
آية رقم 70
ﯻﯼﯽﯾﯿ
ﰀ
Suka ce: "Ashe ba mu hana ka daga tãlikai ba?"
آية رقم 71
ﭑﭒﭓﭔﭕﭖ
ﭗ
Ya ce: "Ga waɗannan, 'ya'yãna idan kun kasance mãsu aikatãwa ne."
آية رقم 72
ﭘﭙﭚﭛﭜ
ﭝ
Rantsuwa da rãyuwarka! Lalle ne sũ a cikin mãyensu sunã ta ɗĩmuwa.
آية رقم 73
ﭞﭟﭠ
ﭡ
Sa'an nan tsãwa ta kãma su, sunã mãsu shiga lõkacin hũdõwar rãnã.
آية رقم 74
Sa'an nan Muka sanya samanta ya kõma ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu na lãkar wuta a kansu.
آية رقم 75
ﭫﭬﭭﭮﭯ
ﭰ
Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu tsõkaci da hankali.
آية رقم 76
ﭱﭲﭳ
ﭴ
Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa sunã a gẽfen wata hanyã tabbatacciya.
آية رقم 77
ﭵﭶﭷﭸﭹ
ﭺ
Lalle ne a cikin wancan akwai ãyã ga mãsu ĩmãni.
آية رقم 78
ﭻﭼﭽﭾﭿ
ﮀ
Kuma lalle ne ma'abũta Al'aika sun kasance, haƙĩƙa, mãsu zãlunci!
آية رقم 79
ﮁﮂﮃﮄﮅ
ﮆ
Sai Muka yi azãbar rãmuwã a gare su, kuma lalle sũ biyun, haƙĩƙa, sunã a gẽfen wani tafarki mabayyani.
آية رقم 80
ﮇﮈﮉﮊﮋ
ﮌ
Kuma lalle ne haƙĩƙa ma'abũta Hijiri sun ƙaryata Manzanni.
آية رقم 81
ﮍﮎﮏﮐﮑ
ﮒ
Kuma Kuka kai musu ãyõyinMu, sai suka kasance mãsu bijirẽwa daga gare su.
آية رقم 82
ﮓﮔﮕﮖﮗﮘ
ﮙ
Kuma sun kasance sunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, alhãli sunã amintattu.
آية رقم 83
ﮚﮛﮜ
ﮝ
Sai tsãwa ta kãma su sunã mãsu shiga asuba.
آية رقم 84
ﮞﮟﮠﮡﮢﮣ
ﮤ
Sa'an nan abin da suka kasance sunã tsirfantãwa bai wadãtar ga barinsu ba.
آية رقم 85
Kuma ba Mu halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu ba fãce da gaskiya. Kuma lalle ne Sã'a (Rãnar Alƙiyãma) haƙĩƙa mai zuwa ce. Sabõdahaka ka yi rangwame, rangwame mai kyau.
آية رقم 86
ﯗﯘﯙﯚﯛ
ﯜ
Lalle ne Ubangijinka, shi ne Mai yawan halitta, Masani.
آية رقم 87
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bã ka bakwai waɗanda ake maimaita karatunsu da Alƙur'ãni mai girma.
آية رقم 88
Kada lalle kaƙĩƙa idãnunka biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi game da shi, nau'i-nau'i a gare su, kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma sassauta fikãfikanka ga mãsu ĩmãni.
آية رقم 89
ﯵﯶﯷﯸﯹ
ﯺ
Kuma ka ce: "Lalle nĩ nĩ ne mai gargaɗi bayyananne."
آية رقم 90
ﯻﯼﯽﯾ
ﯿ
Kamar yadda Muka saukar a kan mãsu yin rantsuwa,
آية رقم 91
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Waɗanda suka sanya Alƙur'ãni tãtsuniyõyi.
آية رقم 92
ﭖﭗﭘ
ﭙ
To, rantsuwa da Ubangijinka! Haƙĩƙa, Munã tambayarsugabã ɗaya.
آية رقم 93
ﭚﭛﭜ
ﭝ
Daga abin da suka kasance sunã aikatãwa.
آية رقم 94
ﭞﭟﭠﭡﭢﭣ
ﭤ
Sai ka tsage gaskiya game da abin da ake umurnin ka kuma ka kau da kai daga masu shirki.
آية رقم 95
ﭥﭦﭧ
ﭨ
Lalle ne Mũ Mun isar maka daga mãsu izgili.
آية رقم 96
Waɗanda suke sanyãwar wani abin bautãwa na dabam tare da Allah, sa'an nan da sannu zã su sani.
آية رقم 97
Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã sanin cẽwa lalle kai, ƙirjinka yanã yin ƙunci game da abin da suke faɗã (na izgili).
آية رقم 98
ﭻﭼﭽﭾﭿﮀ
ﮁ
Sabõda haka ka yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka kasance daga mãsu sujada.
آية رقم 99
ﮂﮃﮄﮅﮆ
ﮇ
Kuma ka bauta wa Ubangijinka, har mutuwa ta zo maka.
تقدم القراءة