ترجمة معاني سورة المدّثر باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﮪﮫ
ﮬ
Al-Muddasir
Yã wanda ya lulluɓa da mayãfi.
آية رقم 2
ﮭﮮ
ﮯ
Ka tãshi dõmin ka yi gargaɗi
آية رقم 3
ﮰﮱ
ﯓ
Kuma Ubangijinka, sai ka girmama Shi,
آية رقم 4
ﯔﯕ
ﯖ
Kuma tutãfinka, sai ka tsarkake su,
آية رقم 5
ﯗﯘ
ﯙ
Kuma gumãka, sai ka ƙaurace musu.
آية رقم 6
ﯚﯛﯜ
ﯝ
Kada ka yi kyauta kana nẽman ƙãri
آية رقم 7
ﯞﯟ
ﯠ
Kuma sabõda Ubangijinka? Sai ka yi haƙure
آية رقم 8
ﯡﯢﯣﯤ
ﯥ
To, idan aka yi bũsa a cikin ƙaho.
آية رقم 9
ﯦﯧﯨﯩ
ﯪ
To, wannan, a rãnar nan, yini ne mai wuya
آية رقم 10
ﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
A kan kãfirai, bã mai sauƙi ba ne.
آية رقم 11
ﯰﯱﯲﯳ
ﯴ
Ka bar Ni da wanda Na halitta, yana shi kaɗai,
آية رقم 12
ﯵﯶﯷﯸ
ﯹ
Kuma Na sanya masa dũkiya shimfiɗaɗɗiya
آية رقم 13
ﯺﯻ
ﯼ
Da ɗiyã halartattu,
آية رقم 14
ﯽﯾﯿ
ﰀ
Kuma Na shimfiɗa? masa kõme shimfiɗãwa.
آية رقم 15
ﰁﰂﰃﰄ
ﰅ
Sa'an nan, yanã kwaɗayin in yi masa ƙãri!
آية رقم 16
ﰆﰇﰈﰉﰊﰋ
ﰌ
Faufau! Lalle ne, shĩ yã kasance, ga ãyõyinMu, mai tsaurin kai.
آية رقم 17
ﰍﰎ
ﰏ
Zã Ni kallafa masa wahala mai hauhawa.
آية رقم 18
ﰐﰑﰒ
ﰓ
Lalle ne, Shi, yã yi tunãni, kuma yã ƙaddara (abin da zai faɗã game da Alƙur'ãni)
آية رقم 19
ﭑﭒﭓ
ﭔ
Sabõda haka, aka la'ane shi, kamar yadda ya ƙaddara.
آية رقم 20
ﭕﭖﭗﭘ
ﭙ
Sa'an nan, aka la'ane shi kamar yadda ya ƙaddara.
آية رقم 21
ﭚﭛ
ﭜ
Sa'an nan, ya yi tunãni
آية رقم 22
ﭝﭞﭟ
ﭠ
Sa'an nan, ya gintse huska? kuma ya yi murtuk.
آية رقم 23
ﭡﭢﭣ
ﭤ
Sa'an nan, ya jũya bãya, kuma ya bunƙãsa,
آية رقم 24
ﭥﭦﭧﭨﭩﭪ
ﭫ
Sai ya ce: "Wannan abu dai bã kõme ba ne fãce wani sihiri, wanda aka ruwaito."
آية رقم 25
ﭬﭭﭮﭯﭰ
ﭱ
"Wannan maganar mutum dai ce."
آية رقم 26
ﭲﭳ
ﭴ
Zã Ni ƙõna shi da Saƙar.
آية رقم 27
ﭵﭶﭷﭸ
ﭹ
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽwa Saƙar!
آية رقم 28
ﭺﭻﭼﭽ
ﭾ
Bã ta ragẽwa, kuma bã ta bari.
آية رقم 29
ﭿﮀ
ﮁ
Mai nãcẽwa ga jiki ce (da (ƙũna).
آية رقم 30
ﮂﮃﮄ
ﮅ
A kanta akwai (matsara) gõma shã tara.
Kuma ba Mu sanya ma'abũta wutã (wãto matsaranta) ba, fãce malã'iku, kuma ba Mu sanya adadinsu (gõma sha tara) ba, fãce dõmin fitina ga waɗanda suka kãfirta domin waɗanda aka bai wa littãfi su sãmi yaƙĩni kuma waɗanda suka yi ĩmãni su ƙãra ĩmãni, kuma waɗanda aka bai wa littãfi da mũminai bã zã su yi shakka ba, kuma domin wa ɗanda a cikin zukatansu akwai wata cuta da kãfirai su ce: "Mẽ Allah Yake nufi da wannan, ya kasance misãli?" Haka dai Allah ke ɓatar da wanda Ya so, kuma Ya shiryar da wanda ya so. Kuma bãbu wanda ya san mayãƙan Ubangijinka fãce Shi, kuma ita (wutar) ba ta kasance ba fãce wata tunãtarwa ce ga mutum.
آية رقم 32
ﯥﯦ
ﯧ
A'aha! Ina rantsuwa da watã.
آية رقم 33
ﯨﯩﯪ
ﯫ
Da dare a lõkacin da ya jũyar da baya.
آية رقم 34
ﯬﯭﯮ
ﯯ
Da sãfiya idan ta wãye.
آية رقم 35
ﯰﯱﯲ
ﯳ
Ita (wutar) ɗayan manyan masĩfũ? ce.
آية رقم 36
ﯴﯵ
ﯶ
Mai gargaɗĩ ce ga mutum.
آية رقم 37
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya gabãta ko ya jinkirta.
آية رقم 38
ﯿﰀﰁﰂﰃ
ﰄ
Kõwane rai ga abin da ya aikata jingina ce.
آية رقم 39
ﰅﰆﰇ
ﰈ
Fãce mutãnen dãma.
آية رقم 40
ﰉﰊﰋ
ﰌ
A cikin Aljanna suna tambayar jũna.
آية رقم 41
ﰍﰎ
ﰏ
Game da mãsu laifi.
آية رقم 42
ﰐﰑﰒﰓ
ﰔ
(Su ce musu) "Me ya shigar da ku a cikin Saƙar?"
آية رقم 43
ﰕﰖﰗﰘﰙ
ﰚ
Suka ce: "Ba mu kasance munã a cikin mãsu salla ba."
آية رقم 44
ﰛﰜﰝﰞ
ﰟ
"Kuma ba mu kasance muna ciyar da matalautã ba."
آية رقم 45
ﰠﰡﰢﰣ
ﰤ
"Kuma mun kasance muna kũtsãwa tãre da mãsu kũtsãwa."
آية رقم 46
ﰥﰦﰧﰨ
ﰩ
"Mun kasance munã ƙaryata rãnar sãkamako."
آية رقم 47
ﰪﰫﰬ
ﰭ
"Har gaskiya (wãto mutuwa) ta zo mana."
آية رقم 48
ﭑﭒﭓﭔ
ﭕ
Sabõda haka cẽton mãsu cẽto bã zai amfãne su ba.
آية رقم 49
ﭖﭗﭘﭙﭚ
ﭛ
Haba! Me ya same su, suka zama mãsu bijirewa daga wa'azin gaskiya.
آية رقم 50
ﭜﭝﭞ
ﭟ
Kamar dai sũ, jãkuna firgitattu ne.
آية رقم 51
ﭠﭡﭢ
ﭣ
Sun gudu daga zãki.
آية رقم 52
A'aha! Kõwãne mutum daga cikinsu yanã son a zo masa da takardu (da sũnansa) ana wãtsãwa
آية رقم 53
ﭮﭯﭰﭱﭲﭳ
ﭴ
A'aha! Kai dai, bã su jin tsõron Lãhira.
آية رقم 54
ﭵﭶﭷ
ﭸ
A'aha! Lalle ne, shi (Alƙur'ãni) tunãtarwa ce.
آية رقم 55
ﭹﭺﭻ
ﭼ
Dõmin wanda ya so, ya tuna.
آية رقم 56
Kuma bã zã su tuna ba fãce idan Allah Ya so, Shi ne Ya cancanta a bi Shi da taƙawa kuma Ya cancanta ga Ya yi gãfara.
تقدم القراءة