ترجمة معاني سورة المدّثر باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

آية رقم 1

Al-Muddasir


Yã wanda ya lulluɓa da mayãfi.
آية رقم 2

Ka tãshi dõmin ka yi gargaɗi
آية رقم 3

Kuma Ubangijinka, sai ka girmama Shi,
آية رقم 4

Kuma tutãfinka, sai ka tsarkake su,
آية رقم 5

Kuma gumãka, sai ka ƙaurace musu.
آية رقم 7

Kuma sabõda Ubangijinka? Sai ka yi haƙure
آية رقم 14

Kuma Na shimfiɗa? masa kõme shimfiɗãwa.
آية رقم 17

Zã Ni kallafa masa wahala mai hauhawa.
آية رقم 18

Lalle ne, Shi, yã yi tunãni, kuma yã ƙaddara (abin da zai faɗã game da Alƙur'ãni)
آية رقم 19

Sabõda haka, aka la'ane shi, kamar yadda ya ƙaddara.
آية رقم 20

Sa'an nan, aka la'ane shi kamar yadda ya ƙaddara.
آية رقم 22

Sa'an nan, ya gintse huska? kuma ya yi murtuk.
آية رقم 23

Sa'an nan, ya jũya bãya, kuma ya bunƙãsa,
آية رقم 24

Sai ya ce: "Wannan abu dai bã kõme ba ne fãce wani sihiri, wanda aka ruwaito."
آية رقم 26

Zã Ni ƙõna shi da Saƙar.
آية رقم 27

Kuma mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽwa Saƙar!
آية رقم 29

Mai nãcẽwa ga jiki ce (da (ƙũna).
آية رقم 30

A kanta akwai (matsara) gõma shã tara.

Kuma ba Mu sanya ma'abũta wutã (wãto matsaranta) ba, fãce malã'iku, kuma ba Mu sanya adadinsu (gõma sha tara) ba, fãce dõmin fitina ga waɗanda suka kãfirta domin waɗanda aka bai wa littãfi su sãmi yaƙĩni kuma waɗanda suka yi ĩmãni su ƙãra ĩmãni, kuma waɗanda aka bai wa littãfi da mũminai bã zã su yi shakka ba, kuma domin wa ɗanda a cikin zukatansu akwai wata cuta da kãfirai su ce: "Mẽ Allah Yake nufi da wannan, ya kasance misãli?" Haka dai Allah ke ɓatar da wanda Ya so, kuma Ya shiryar da wanda ya so. Kuma bãbu wanda ya san mayãƙan Ubangijinka fãce Shi, kuma ita (wutar) ba ta kasance ba fãce wata tunãtarwa ce ga mutum.
آية رقم 32

A'aha! Ina rantsuwa da watã.
آية رقم 33

Da dare a lõkacin da ya jũyar da baya.
آية رقم 35

Ita (wutar) ɗayan manyan masĩfũ? ce.
آية رقم 36

Mai gargaɗĩ ce ga mutum.
آية رقم 45

"Kuma mun kasance muna kũtsãwa tãre da mãsu kũtsãwa."
آية رقم 47

"Har gaskiya (wãto mutuwa) ta zo mana."
آية رقم 48

Sabõda haka cẽton mãsu cẽto bã zai amfãne su ba.
آية رقم 49

Haba! Me ya same su, suka zama mãsu bijirewa daga wa'azin gaskiya.
آية رقم 54

A'aha! Lalle ne, shi (Alƙur'ãni) tunãtarwa ce.
تقدم القراءة