ترجمة معاني سورة القلم باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation

آية رقم 1

Al-Kalam


Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.
آية رقم 4

Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.
آية رقم 5

Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.
آية رقم 8

Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.
آية رقم 13

Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).

Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
آية رقم 18

Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
آية رقم 19

Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
آية رقم 20

Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.
آية رقم 21

Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.
آية رقم 23

Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).
آية رقم 25

Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.
آية رقم 26

Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"
آية رقم 29

Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."
آية رقم 31

Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."

"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."
آية رقم 34

Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.
آية رقم 35

Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?
آية رقم 38

Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?
آية رقم 40

Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?
آية رقم 41

Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.

Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).
آية رقم 46

Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?
آية رقم 47

Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?

Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.

Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.
آية رقم 50

Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.

Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"
آية رقم 52

Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.
تقدم القراءة