ترجمة معاني سورة القلم باللغة الهوساوية من كتاب Abubakar Mahmoud Gumi - Hausa translation
ﰡ
آية رقم 1
ﮉﮊﮋﮌﮍ
ﮎ
Al-Kalam
Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.
آية رقم 2
ﮏﮐﮑﮒﮓ
ﮔ
Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.
آية رقم 3
ﮕﮖﮗﮘﮙ
ﮚ
Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.
آية رقم 4
ﮛﮜﮝﮞ
ﮟ
Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.
آية رقم 5
ﮠﮡ
ﮢ
Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.
آية رقم 6
ﮣﮤ
ﮥ
Ga wanenku haukã take.
آية رقم 7
Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.
آية رقم 8
ﯓﯔﯕ
ﯖ
Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.
آية رقم 9
ﯗﯘﯙﯚ
ﯛ
Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.
آية رقم 10
ﯜﯝﯞﯟﯠ
ﯡ
Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.
آية رقم 11
ﯢﯣﯤ
ﯥ
Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.
آية رقم 12
ﯦﯧﯨﯩ
ﯪ
Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.
آية رقم 13
ﯫﯬﯭﯮ
ﯯ
Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).
آية رقم 14
ﯰﯱﯲﯳﯴ
ﯵ
Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.
آية رقم 15
Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."
آية رقم 16
ﯾﯿﰀ
ﰁ
Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.
آية رقم 17
Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
آية رقم 18
ﭜﭝ
ﭞ
Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
آية رقم 19
Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
آية رقم 20
ﭧﭨ
ﭩ
Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.
آية رقم 21
ﭪﭫ
ﭬ
Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.
آية رقم 22
Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.
آية رقم 23
ﭵﭶﭷ
ﭸ
Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).
آية رقم 24
ﭹﭺﭻﭼﭽﭾ
ﭿ
"Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"
آية رقم 25
ﮀﮁﮂﮃ
ﮄ
Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.
آية رقم 26
ﮅﮆﮇﮈﮉ
ﮊ
Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"
آية رقم 27
ﮋﮌﮍ
ﮎ
"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."
آية رقم 28
Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"
آية رقم 29
ﮗﮘﮙﮚﮛﮜ
ﮝ
Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."
آية رقم 30
ﮞﮟﮠﮡﮢ
ﮣ
Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.
آية رقم 31
ﮤﮥﮦﮧﮨ
ﮩ
Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."
آية رقم 32
"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."
آية رقم 33
Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.
آية رقم 34
ﯡﯢﯣﯤﯥﯦ
ﯧ
Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.
آية رقم 35
ﯨﯩﯪ
ﯫ
Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?
آية رقم 36
ﯬﯭﯮﯯ
ﯰ
Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?
آية رقم 37
ﯱﯲﯳﯴﯵ
ﯶ
Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?
آية رقم 38
ﯷﯸﯹﯺﯻ
ﯼ
Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?
آية رقم 39
Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?
آية رقم 40
ﰊﰋﰌﰍ
ﰎ
Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?
آية رقم 41
Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.
آية رقم 42
Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba.
آية رقم 43
Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).
آية رقم 44
Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.
آية رقم 45
ﭪﭫﭬﭭﭮﭯ
ﭰ
Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne.
آية رقم 46
Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?
آية رقم 47
ﭹﭺﭻﭼﭽ
ﭾ
Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?
آية رقم 48
Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.
آية رقم 49
Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.
آية رقم 50
ﮖﮗﮘﮙﮚ
ﮛ
Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.
آية رقم 51
Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"
آية رقم 52
ﮩﮪﮫﮬﮭ
ﮮ
Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.
تقدم القراءة